• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Kotun Shari’ar Musulunci Ta Tura Sheikh Idris Abdul’aziz Gidan Yari

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Da Dumi-Dumi: Kotun Shari’ar Musulunci Ta Tura Sheikh Idris Abdul’aziz Gidan Yari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci mai lamba 1 da ke Jihar Bauchi ta tura Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi gidan yari bisa ‘raini ga kotu’ har zuwa nan da wata daya.

Alkalin kotun, Malam Hussaini Turaki, shi ne ya aike da babban malamin zuwa gidan gyara halinka a zaman kotun da ya gudana ranar Litinin.

  • Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi

A kwafin umurnin aikewa da Malamin gidan yari da wakilinmu ya ci karo da ita da ke nuni da cewa bisa ga ‘raini ga kotu’ wato ‘Contempt of court’ ne Alkalin ya aike da malamin gidan yari, inda za a da dawo da shi gaban kotun a ranar 19 ga watan gobe.

Umurnin da Alkalin ya bai wa babban jami’in kula da gidan yarin na cewa, “An baka izinin ka karbe shi ka tsare shi a gadirum sai an aiko maka da wata oda.”

Umarnin na kotun ya ce idan har ba wata umarnin na daban kuma aka aiko ba, malamin zai cigaba da zama a gidan har zuwa ranar 19/07/2023.

Labarai Masu Nasaba

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

Idris Abdul'aziz
Takardar shaidar kotun da ta tura Dr. Idris Abdulaziz gidan yari

Idan za a tuna dai, a ranar Laraba 31 ga watan Mayun 2023 ne dai Alkalin kotun ya umarci jami’an tsaro da su kamo malamin a duk inda suka gan shi sakamakon kin bayyana a gaban kotu.

Sai dai a zaman kotun a ranar 5 ga watan Yuni malamin ya bayyana a gaban alkalin inda lauyoyinsa suka gabatar da rahoton likita da ke cewa bai zo kotun ba ne sakamakon rashin lafiya da ke fama da ita.

Bayan da lauyoyin nasa suka gabatar da rahoton, sun roki kotun da ta janye tare da jingine umarnin da ta bayar na farko na cewa a kamo malamin duk aka gan shi. Sai dai Alkalin ya daga zaman zuwa yau don yanke hukunci kan bukatar.

Da yake zantawa da ‘yan jarida bayan hukunci, daya daga cikin Lauyoyin malamin, Barista Kamal A. R Muhammad, ya ce, su na nazarin halin da ake ciki domin daukan matakin da ya dace na nema wa malamin ‘yanci.

A cewarsa: “Da farko an dawo kotun ne domin a saurari bukatarmu na neman a kori karar saboda da hujjarmu na cewa kotun ba ta da hurumin sauraron karar. Na biyu kuma akwai rokon da muka yi na cewa umarnin da kotun ta yi a ranar farko na a nemo malam a tsareshi saboda bai zo kotu ba a jingine don mun gabatar da rahoton asibiti da ke cewa baya da lafiya.

“Kafin yau din ma, mun shigar da daukaka kara da muke neman a canza shari’ar zuwa wata kotu da take da hurumi zuwa gaban alkalin da ke da hurumi, sai Alkalin ya ce ba zai kori karar ba don yana da hurumin sauraron wannan karar.”

A cewar Lauyan, “Yanzu dai halin da ake ciki Alkalin ya ce a kai Malam zuwa gidan yari har zuwa ranar 19 ba watan Yulin 2023.”

Barista Kamal malamin ya ce akwai matakan da za su dauka na nuna korafinsu kan wannan lamarin.

LEADERSHIP Hausa ta yi tilawar cewa, tun da farko dai, ‘yansanda ne suka fara gabatar da malamin a kotun majistire bisa zarginsa da laifin tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiyan al’umma, lamarin da ya kai ga zuwansa gidan yari na tsawon mako guda amma daga bisani ya samu beli.

Kodayake ma’aikatar shari’a ta Jihar Bauchi ta amshi ragamar shari’ar daga baya.

Sai dai kuma bayan fitowarsa ne aka sake mayar da shari’ar da ake masa daga kotun majistiren zuwa kotun shari’ar Musulunci.

Wakilinmu ya ce, zuwa yanzu haka dai malamin wanda shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi na tsare a babban gidan gyara halin da ke Bauchi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugaba Xi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Next Post

Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

Related

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

3 hours ago
Idris Abdul'aziz
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

4 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

5 hours ago
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

8 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

11 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

11 hours ago
Next Post
Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

June 7, 2025
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

June 7, 2025
Idris Abdul'aziz

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

June 7, 2025
Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

Tottenham Ta Raba Gari Da Kocinta Ange Postecoglu

June 7, 2025
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

June 7, 2025
Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.