ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Kotun Shari’ar Musulunci Ta Tura Sheikh Idris Abdul’aziz Gidan Yari

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Idris Abdul'aziz

Babbar Kotun Shari’ar Musulunci mai lamba 1 da ke Jihar Bauchi ta tura Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi gidan yari bisa ‘raini ga kotu’ har zuwa nan da wata daya.

Alkalin kotun, Malam Hussaini Turaki, shi ne ya aike da babban malamin zuwa gidan gyara halinka a zaman kotun da ya gudana ranar Litinin.

  • Wakili Ya Rasu Kwana 3 Da Karewar Wa’adinsa A Matsayin Dan Majalisar Dokokin Jihar Bauchi

A kwafin umurnin aikewa da Malamin gidan yari da wakilinmu ya ci karo da ita da ke nuni da cewa bisa ga ‘raini ga kotu’ wato ‘Contempt of court’ ne Alkalin ya aike da malamin gidan yari, inda za a da dawo da shi gaban kotun a ranar 19 ga watan gobe.

ADVERTISEMENT

Umurnin da Alkalin ya bai wa babban jami’in kula da gidan yarin na cewa, “An baka izinin ka karbe shi ka tsare shi a gadirum sai an aiko maka da wata oda.”

Umarnin na kotun ya ce idan har ba wata umarnin na daban kuma aka aiko ba, malamin zai cigaba da zama a gidan har zuwa ranar 19/07/2023.

LABARAI MASU NASABA

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Idris Abdul'aziz
Takardar shaidar kotun da ta tura Dr. Idris Abdulaziz gidan yari

Idan za a tuna dai, a ranar Laraba 31 ga watan Mayun 2023 ne dai Alkalin kotun ya umarci jami’an tsaro da su kamo malamin a duk inda suka gan shi sakamakon kin bayyana a gaban kotu.

Sai dai a zaman kotun a ranar 5 ga watan Yuni malamin ya bayyana a gaban alkalin inda lauyoyinsa suka gabatar da rahoton likita da ke cewa bai zo kotun ba ne sakamakon rashin lafiya da ke fama da ita.

Bayan da lauyoyin nasa suka gabatar da rahoton, sun roki kotun da ta janye tare da jingine umarnin da ta bayar na farko na cewa a kamo malamin duk aka gan shi. Sai dai Alkalin ya daga zaman zuwa yau don yanke hukunci kan bukatar.

Da yake zantawa da ‘yan jarida bayan hukunci, daya daga cikin Lauyoyin malamin, Barista Kamal A. R Muhammad, ya ce, su na nazarin halin da ake ciki domin daukan matakin da ya dace na nema wa malamin ‘yanci.

A cewarsa: “Da farko an dawo kotun ne domin a saurari bukatarmu na neman a kori karar saboda da hujjarmu na cewa kotun ba ta da hurumin sauraron karar. Na biyu kuma akwai rokon da muka yi na cewa umarnin da kotun ta yi a ranar farko na a nemo malam a tsareshi saboda bai zo kotu ba a jingine don mun gabatar da rahoton asibiti da ke cewa baya da lafiya.

“Kafin yau din ma, mun shigar da daukaka kara da muke neman a canza shari’ar zuwa wata kotu da take da hurumi zuwa gaban alkalin da ke da hurumi, sai Alkalin ya ce ba zai kori karar ba don yana da hurumin sauraron wannan karar.”

A cewar Lauyan, “Yanzu dai halin da ake ciki Alkalin ya ce a kai Malam zuwa gidan yari har zuwa ranar 19 ba watan Yulin 2023.”

Barista Kamal malamin ya ce akwai matakan da za su dauka na nuna korafinsu kan wannan lamarin.

LEADERSHIP Hausa ta yi tilawar cewa, tun da farko dai, ‘yansanda ne suka fara gabatar da malamin a kotun majistire bisa zarginsa da laifin tada zaune tsaye da ke barazana ga zaman lafiyan al’umma, lamarin da ya kai ga zuwansa gidan yari na tsawon mako guda amma daga bisani ya samu beli.

Kodayake ma’aikatar shari’a ta Jihar Bauchi ta amshi ragamar shari’ar daga baya.

Sai dai kuma bayan fitowarsa ne aka sake mayar da shari’ar da ake masa daga kotun majistiren zuwa kotun shari’ar Musulunci.

Wakilinmu ya ce, zuwa yanzu haka dai malamin wanda shi ne babban limamin masallacin Juma’a na Dutsen Tanshi na tsare a babban gidan gyara halin da ke Bauchi.

Idris Abdul'aziz
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara
Rahotonni

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15
Labarai

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Next Post
Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

Maimakon Yaki, Afirka Da Sin Sun Zabi Zaman Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.