• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Zai Tafi Portugal Yau Talata Don Halartar Taron Majalisar Dinkin Duniya

by Muhammad
3 years ago
in Labarai
0
Buhari Ya Sake Shillawa Kasar Ghana Don Halartar Taron ECOWAS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, zai bar Abuja a yau Talata zuwa ziyarar aiki kasar Portugal bisa gayyatar da shugaban kasar, Marcelo Rebelo de Sousa, ya yi masa, kamar yadda fadar shugaban kasar ta bayyana.

Shugaban wanda zai yi wata tattaunawa a hukumance da takwaransa na Portugal, za kuma a ba shi lambar yabo ta kasa da kuma yi masa ado da ‘Great Collar of the Order of Prince Henry’.

  • Buhari Ya Rantsar Da Ariwoola A Matsayin Sabon Alkalin Alkalai Na Kasa
  • Buhari Ya Ce Ba Zai Nemi Wa’adi Na Uku Ba

Wata sanarwa da mai taimaka wa shugaban kasa na musamman kan harkokin yada labarai, Garba Shehu, ya sanya wa hannu a ranar Talata, ta ce ana sa ran shugabannin biyu za su jagoranci wani gagarumin taron kasashen biyu da kulla wasu yarjeniyoyin da suka shafi kan iyakokin kasashen biyu.

Shugaba Buhari zai kuma ziyarci majalisar dokokin kasar Portugal inda zai tattauna da shugabanta Dr Augusto Santo Silva da kuma firaministan kasar Portugal Antonio Costa.

Shehu ya bayyana cewa, a yayin ziyarar, shugaban kasar zai yi jawabi a wani taron ‘yan kasuwan Nijeriya da na kasar Portugal tare da yin ganawa daban-daban da wasu zababbun manyan jami’an gudanarwa na kasar Portugal da masu son zuba jari a Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

Shugaba Buhari zai kuma halarci taron Majalisar Dinkin Duniya a kan teku, wanda aka fara a Lisbon a ranar Litinin, 27 ga watan Yuni, wanda zai gudana har zuwa 1 ga watan Yuli.

Taron, wanda gwamnatocin Kenya da Portugal suka shirya tare da goyon bayan Sashen Tattalin Arziki da Al’uma na Majalisar Ɗinkin Duniya (DESA), na da nufin hanzarta ɗaukar sabbin hanyoyin samar da sabbin hanyoyin kimiyya don fuskantar ƙalubalen da ke fuskantar teku da kuma yanayin ruwa na duniya.

Ana kuma sa ran shugaban na Nijeriya zai tattauna da ‘yan Nijeriya mazauna kasar Portugal kan al’amuran da suka shafe su da kuma abubuwan da ke faruwa a cikin gida.

Shugaban kasar zai samu rakiyar ministan harkokin waje, Geoffrey Onyeama da Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed da Ministan Masana’antu, Kasuwanci da Zuba Jari, Adeniyi Adebayo sai Ministan Matasa da Wasanni, Sunday Dare da kuma Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami.

Sauran sun hada da mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Maj-Gen Babagana Monguno (rtd) da Darakta Janar na Hukumar Leken Asiri ta Kasa (NIA), Amb. Ahmed Rufa’i Abubakar da shugaban hukumar ‘yan Nijeriya mazauna kasashen waje (NiDCOM) Honorabul Abike Dabiri-Erewa.

Sanarwar ta kara da cewa shugaban zai koma Abuja ranar Asabar 2 ga watan Yuli.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariPortugalShugaba Buharitafiya
ShareTweetSendShare
Previous Post

PDP Ta Ja Kunnen Tsohon Shugaban Kasa, Obasanjo Kan Dan Takararta

Next Post

Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

Related

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato
Labarai

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

18 minutes ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

2 hours ago
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
Labarai

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

3 hours ago
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci
Ra'ayi Riga

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

4 hours ago
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
Labarai

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

4 hours ago
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
Labarai

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

5 hours ago
Next Post
Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

Ranar Laraba Za A Fara Duban Watan Zul-hijjah A Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

Ɗan Majalisa Ya Tallafawa Mata 400 A Sakkwato

May 11, 2025
Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

May 11, 2025
Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

INEC Na Samun Matsin Lamba Don Kar Ta Yi Wa TNN Rajista — Kakakinta

May 11, 2025
Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa

May 11, 2025
Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

Uwargidan Jonathan Ta Bayyana Goyon Bayanta Ga Remi Tinubu

May 11, 2025
Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

Bil’Adama Zai Iya Tabbatar Da Kyakkyawar Makoma Ne Kadai Idan Ya Rike Tarihi A Zuci

May 11, 2025
Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

Sin Na Fatan India Da Pakistan Za Su Kaucewa Kara Rura Wutar Tashin Hankali

May 11, 2025
Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU

May 11, 2025
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

May 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.