• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mene Ne Ma’anar Sakon Xi Jinping Kan Zagayowar Ranar Kafuwar JKS?

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Mene Ne Ma’anar Sakon Xi Jinping Kan Zagayowar Ranar Kafuwar JKS?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ranar 1 ga watan Yuli ne aka cika shekaru 102 da kafuwar Jam’iyyar Kwaminis ta Kasar Sin wato JKS. A daidai lokacin da ake bikin wannan rana, babban sakataren kwamitin tsakiyar JKS, shugaban kasa, kana, shugaban kwamitin soja na kasar Sin, Xi Jinping ya bukaci a warware matsalar musamman dake gaban jam’iyyar, da kyautata tsarin gudanarwar harkokin jam’iyyar daga dukkan fannoni, da kara kwarewar aikin jami’an kasar, ta yadda za su ba da gudummawa wajen farfado da al’ummar Sinawa baki daya. Mene ne ma’anar sakon da Xi Jinping ya bayar, kuma mene ne alakar mulkin jam’iyya da na kasa?

Duk wanda ya fahimci tarihin kasar Sin ya san cewa, tarihin kasar Sin cikin shekaru 100 da suka gabata, ba a iya raba shi da jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ba, kuma tasowa ko faduwar kasar yana da alaka da jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin. A cikin shekaru 100 da suka gabata, nasarar da JKS ta samu ya dogara ne kan jagoranci mai karfi, raya kanta, da gudanar da ayyukanta yadda ya kamata.

A halin yanzu, Xi na ci gaba da jagorantar aikin yin kwaskwarima ga JKS, ya kuma tsaya tsayin daka wajen gudanar da ayyukan JKS bisa tsari, da yin kwaskwarima, domin warware matsala ta musamman dake gaban wannan babbar jam’iyya a duniya, ta yadda jam’iyyar za ta ci gaba da ba da jagoranci ga kasar Sin, a kokarin wadatar da al’ummar ta, da neman farfadowar kasar Sin, gami da shimfida zaman lafiya mai dorewa, da tabbatar da jin dadin al’umomin duniya baki daya.

Xi Jinping na mai da matukar hankali kan gudanarwar harkokin JKS, inda ya bukaci a gudanar da harkokin JKS kamar yadda aka tsara a dukkan fannoni, kuma, ya hada wannan bukata tare da aikin gina kasa mai tsarin gurguzu ta zamani a dukkan fannoni, da zurfafa aikin kwaskwarima a dukkan fannoni, da gudanar da ayyukan kasa bisa doka a dukkan fannoni, wadanda suka kasance babbar manufa da babban tsarin gudanar da harkokin kasar Sin, lamarin da ya nuna dangantakar dake tsakanin JKS da aikin zamanintar da kasa, wayewar kan kasa, farfadowar kasa. Ma’ana, bin jagorancin JKS shi ne tushen gudanar da harkokin kasa kamar yadda ake fata. (Mai Fassarawa: Maryam Yang)

 

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Sallah

Next Post

Kura Ta Turnike Majalisar Dattawa Kan Nadin Shugaban Marasa Rinjaye

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

6 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

6 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

7 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

9 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

10 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

12 hours ago
Next Post
gaza

Kura Ta Turnike Majalisar Dattawa Kan Nadin Shugaban Marasa Rinjaye

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.