ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, July 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kura Ta Turnike Majalisar Dattawa Kan Nadin Shugaban Marasa Rinjaye

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
gaza

Kura ta turnike zauren majalisar dattawa kan gwagwarmayar neman mukamin shugaban marasa rinjaye.

Kurar ta turnike ne bayan da rikicin kujerar shugaban marasa rinjaye na majalisar dattawa ya haifar da rashin jituwa a tsakanin sanatocin ‘yan jam’iyyar adawa na kokarin kaka ba musu shugabancin.

  • Hajji 2023: Tinubu Ya Bukaci Alhazai Da Su Kara Hakuri Da Halin Matsi Da Takura Da Suke Ciki

A majalisar dattawa ta 10, APC tana da sanatoci 59, PDP tana da 36, LP tana da 8, SDP na da 2, NNPP tana da 2, YPP na da 1, APGA na da 1.

ADVERTISEMENT

Manyan mukamai hudu da aka ware wa jam’iyyun adawa a Majalisar Dattawa su ne, shugaban marasa rinjaye, mataimakin shugaban marasa rinjaye, mai tsawatarwa na marasa rinjaye da mataimakin mai tsawatarwa.

A wani yunkuri na samun hadil kai abokansa a matsayin shugaban marasa rinjaye a zauren majalisar dattawa, tsohon gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Wike ya gana da Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio a ranar Alhamis da ta gabata.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

Ganawar ya gudana ne a zauren majalisar na tsawan awanni da dama. Wike ya bar majalisar ne da misalin karfe 6:30 na yamma ba tare da ya yi magana da manema labarai ba.

An ce tsohon gwamnan Jihar Ribas ya bukaci abokinsa, Kingsley Chinda a matsayin shugaban marasa rinjaye a majalisar wakilai, duk da cewa har yanzu ba a tabbatar da shi ba.

Sai dai PDP da ke da kujeru mafi rinjaye a ‘yan majalisar dattawa 36 daga cikin jam’iyyun adawa, ta sha alwashin yin tir da duk wani makirci da jam’iyyar APC mai mulki ko wasu masu ruwa da tsaki za su yi na kulla alaka da ‘yan tsiraru a majalisar dattawa domin nada shugaban marasa rinjaye.

Har ila yau, ‘yan majalisar daga bangaren ‘yan adawar sun ce suna sane da matakin kutse a ciki da wajen majalisar dattawa ake yi na raba kan ‘yan tsirarun jam’iyyu da kuma samar musu da shugabancin da bai dace ba. Duk da haka, sun ba da tabbacin cewa makircin ba zai yi tasiri ba.

Da yake zantawa da Jaridar Daily Trust a jiya, Sakataren yada labarai na jam’iyyar PDP na kasa, Debo Ologunagba, ya ce ‘yan Nijeriya sun tabbatar da cewa jam’iyyar PDP tare da sanatocinta za su kafa wasu tsirarun shugabannin da za su tabbatar da raba madafun iko da kuma tantancewa.

Ya ce, “Jam’iyyarmu jam’iyya ce take da tsari kuma muna bin ka’idojinmu. A kan batun shugabancin marasa rinjaye a Majalisar Dattawa, PDP na tuntubar sanatocinta bisa tsarin dimokuradiyyarmu.

“Abin da ya fi dacewa a gare mu a jam’iyya shi ne, samun shugabancin masara rinjaye da zai tabbatar da tsayayyen adawa a majalisar dattawa da kuma maslahar ‘yan Nijeriya baki daya.

“Za mu mai da hankali kan tabbatar da cewa an bi tsarin dimokuradiyya da kuma ka’idojin raba madafun iko. Muna tuntubar jama’armu kuma bayaninsu ya yi daidai da matsayinmu na jam’iyya, muna tattaunawa da su, kuma a karshe za mu fitar da matsayinmu na samun tsayuwar adawa mai karfi a cikin majalisar kasa.

“Za mu tabbatar an bi ka’idojin tsarin mulki,” in ji shi.

Tun a ranar Asabar da ta gabata, ‘yan majalisar dattawa daga jam’iyyun adawa sun sha alwashin yin fatali da duk wani yunkuri na dora musu shugaban marasa rinjaye wanda bai dace ba a zauren majalisar dattawa.

A cikin wata sanarwar hadin gwiwa na ‘yan majalisar da suka fitar sun ce ‘yan adawa za su zabi shugabanninsu ne bayan tattaunawa da jam’iyyun siyasarsu ba tare da tsangwama daga masu yin kutse ga tsarin dimokuradiyya ba.

Sun jadadda cewa har yanzu babu wani sanata da aka amince da shi ko aka zaba a matsayin shugaban marasa rinjaye.

Sanarwar ta samu sa hannun hadin gwiwar Mohammed Adamu Aliero, Henry Seriake Dickson, Aminu Waziri Tambuwal, Abdul Ningi, Patrick Abba Moro, Ezenwa Francis Onyewuchi, Sumaila Kawu da kuma Ifeanyi Patrick Ubah.

Ta ci gaba da cewa, “Ga zuwa yanzu dai, ‘yan jam’iyyun adawa a zauren Majalisar Dattawan ana kokarin raba kan ‘yan adawa kuma yi musu zagon-kasa wajen kakaba musu shugabanni.

“Mun yi alkawarin yin aiki tare da sabbin shugabannin majalisar dattawa da bangaren zartarwa don isar da kyakkyawan shugabanci ga al’ummar Nijeriya. Don haka muna ba da shawara da lura cewa ka da su taimaka wa wata kungiya a ciki ko wajen majalisar dattawa don raba kan ‘yan adawa.

“Sanatocin jam’iyyun adawa za su gana idan majalisar dattawa ta dawo daga hutu, kuma za mu tuntubi jam’iyyun siyasarmu wajen zaben shugabanninmu ba tare da tsangwama daga masu kutse a dimokuradiyya a ciki ko wajen majalisar dattawa ba.

“Don kauce wa shakku, har yanzu babu wani sanata da aka amince da shi ko aka zaba a matsayin shugaban marasa rinjaye saboda bin tsarin da ya dace kamar yadda dukkanin ‘yan dawa suka amince a taronsu na karshe.

“Ba za lamunci duk wani yunkurin kafa mulkin kama-karya na jam’iyya mai mulki ba.
“Muna kira ga dukkan ‘yan jam’iyyun siyasa marasa rinjaye da su yi aiki tare cikin hadin kai don kare tsarin dimokuradiyya na majalisar dattawa da na Nijeriya.”

Majalisar Dattawa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

MASU ALAKA

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Tinubu Da Atiku Da Obi Na Ci Gaba Da Zafafa Neman Kuri’un Arewacin Nijeriya

July 17, 2026
Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura
Tambarin Dimokuradiyya

Zaben 2027:Tikitin Muslim-muslim Na Jam’iyyar APC Ya Sake Tayar Da Kura

July 17, 2026
‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Next Post
JKS Tana Da Mambobi Sama Da Miliyan 98 Ya Zuwa Karshen 2022

JKS Tana Da Mambobi Sama Da Miliyan 98 Ya Zuwa Karshen 2022

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

Sojoji Sun Daƙile Yunƙurin ISWAP Na Sace Ɗalibai A Borno, Sun Ceto 46

July 19, 2026
Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

Ba Mu Sayar Wa Dangote Da Reshen Jami’ar SAZU Na Yuli Ba-Gwamnatin Bauchi

July 19, 2026
Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ta Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Asibitin Burkina Faso

July 19, 2026
NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

NDLEA Ta Cafke Kwayoyin Tramadol Miliyan 1.63 Da Akai Nufin Shigar Da Su Kano

July 19, 2026
Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

Ra’ayin Sin Game Da AI Mai Mayar Da Hankali Kan Bukatun Dan Adam Ya Samu Goyon Bayan Kasa Da Kasa

July 19, 2026
Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

Kada A Bar Kasashe Masu Tasowa A Baya A Zamanin AI

July 19, 2026
Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

Gwamna Radda Ya Kaddamar da Tattaunawar Kasafin Kuɗin 2027

July 19, 2026
Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

Shugaba Tinubu Zai Yi Jawabi Ga Shugabannin Duniya A Taron MDD Karo Na 81

July 19, 2026
majalisar kasa

Damawa Da Mata A Siyasa: Kujerun Majalisun Tarayya Na Iya Ƙaruwa Zuwa 121, da Kuma 397 A 2027

July 19, 2026
Kofin Duniya

Abubuwa Uku Da Ya Kamata Kusani Akan Kofin Duniya

July 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.