• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Yan Nijeriya Sun Damu Kan Yadda Kayan Masarufi Ke Tashin Gwauron Zabi

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
‘Yan Nijeriya Sun Damu Kan Yadda Kayan Masarufi Ke Tashin Gwauron Zabi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

‘Yan Nijeriya sun damu da halin da suka tsinci kansu na ci gaba da fuskantar hauhawan farashin kayan abinci. 

Hukumar kididdiga ta kasa (NBS) ta bayyana cewa hauhawar farashin kayan abinci daga shekara zuwa shekara na kara ta’azzara.

  • Kotu Ta Daure Wata Mata Kan  Zargin Kashe Mijinta A Oyo
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Manomi A Nasarawa

A cewar NBS, hauhawar farashin kayan abinci, ya karu da kashi 22.22 a cikin dari a cikin watan Afirilun 2023.

A baya farashin kwandon tumaturi ya kai daga Naira 90,000 zuwa Naira 100,000, sabanin yadda a baya ake sayar da kwandon sa daya akan Naira 20,000.

Har ila yau, farashin kwandon tattasai wanda a baya ake sayarwa akan Naira 12,000 zuwa Naira 15,000, a yanzu ana sayar da shi Naira 40,000 zuwa Naira 45,000.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

Sauran kayan abincin kamar su taliyar leda mai dauke da guda 20 duk katan daya ana sayar da ita kan Naira 10,200.

Haka taliyar ‘yan yara mak dauke da guda 40 a cikin leda, ana sayar da duk katan daya kan Naira 8,000.

Baya ga hauhawar farashin kayan abincin da ake ci gaba da fuskanta, an kuma danganta tashin gwaron zabin kayan abincin akan tsadar farashin man fetur da faduwar darajar Naira da kuma karancin kayan aikin gona.

Wadannan matsalolin da aka zayyano, kari da kalubalen rashin tsaro a kasar nan sun kara jefa musamman talakawan kasar nan a cikin halin kuncin rayuwa.

A daya bangaren, wasu daga cikin manoman kasar nan, na ci gaba da fuskantar tsadar farashin kayan aikin noma, musamman saboda tsadar farashin takin zamani da magungunan kashe kwari da rashin samun ingantaccen irin noma da kuma rashin samar masu da kyayawan tsari, don yin noman rani.

Wani magidanci dan shekara 47 mai suna Emmanuel Ikechukwu da ke zaune a yankin Orozo da ke Abuja, wanda kuma yake da iyalai shida, ya bayyana cewa wannan ne karo na farko a rayuwarsa da ya taba fuskantar matsin ruyuwa da ta hade masa da hauhawar farashin kayan abinci da tsadar sufuri.

Wasu magidantan na ta hakilon samar wa iyalansu abin da za su ci, amma farashin kayan abincin, sai kara hauhawa yake yi.

Wasu gidajen da dama sun rage yawan kayan abincin da suke sayawa ahalinsu, haka sun dakatar da sayen manya kayan more rayuwa da suka saba siya.

Wani malamin makaranta mai suna Mallam Abubakar Usman, wanda ke zaune a yankin Karu a Abuja, shi ma kokawa ya yi akan hauhawan farashin kayan abincin.

Abubakar, ya ce “A yanzu haka ni da dan uwana, muna tsallake cin abinci har da ‘ya’yana uku saboda tashin gwaron zabin na kayan masarufin.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kayan MasarufiTashin Gwauron ZabiTsadar Rayuwa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kotu Ta Daure Wata Mata Kan  Zargin Kashe Mijinta A Oyo

Next Post

Ana Rade-Radin Bullar Cutar ‘Diphtheria’ A Garin Potiskum Na Jihar Yobe

Related

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

3 hours ago
Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

7 hours ago
Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya
Manyan Labarai

Gwamnan Neja Ya Kori Kwamishinoninsa Gaba ÆŠaya

11 hours ago
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai
Manyan Labarai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

15 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

16 hours ago
An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 
Manyan Labarai

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 

1 day ago
Next Post
Matsalolin Tsaro Sun Kusa Zama Tarihi A Nijeriya– Gwamna Buni

Ana Rade-Radin Bullar Cutar 'Diphtheria' A Garin Potiskum Na Jihar Yobe

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

Xi Ya Gabatar Da Shawarar Tsarin Shugabanci Na Duniya 

September 1, 2025
Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

Peng Liyuan Da Matan Shugabannin Kasashe Membobin SCO Masu Halartar Taron SCO Sun Ziyarci Kogin Haihe Na Tianjin

September 1, 2025
Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

Tottenham Ta Dauki Aron Kolo Muani Daga PSG

September 1, 2025
AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

AU: Hadin Gwiwar Sin Da Afirka A Fannin Bunkasa Noma Na Da Matukar Muhimmanci

September 1, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Ƙarin Kasafin Naira Biliyan 215.3 A Na 2025

September 1, 2025
Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

Shugaban Zimbabwe Ya Sauka Beijing Domin Halartar Bikin Cika Shekaru 80 Da Cimma Nasarar Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan

September 1, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

September 1, 2025
Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

September 1, 2025
NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

September 1, 2025
Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

Antonio Guterres: Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

September 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.