ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, July 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Na Shiri Da Ƴan Bindiga, Tana Ba Su Biliyoyi — El-Rufai

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
Tarayya

Tsohon gwamnan Jihar Kaduna kuma tsohon Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Malam Nasir El-Rufai, ya zargi gwamnatin tarayya da zaɓar hanya biyan kuɗaɗe da samar da kayan tallafi ga ƴan bindiga ƙarƙashin abin da ake kira dabarar “non-kinetic” wajen yaƙi da rashin tsaro. Ya bayyana cewa wannan tsari ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan tsaro (ONSA) ne ke jagoranta, tare da jaddada cewa akwai hujjojin tabbatar da hakan.

A yayin tattaunawa a shirin Sunday Politics na gidan talabijin ɗin Channes, El-Rufai ya bayyana cewa gwamnati na bai wa ƴan bindiga kuɗi da kayan abinci, lamarin da ya kira “tallafa wa ta’addanci”. Ya ce ba zai taɓa amincewa da irin wannan dabarar ba. “Abin da ba zan taɓa yi ba shi ne in biya ƴan bindiga, in riƙa ba su tallafi na kudi da abinci da sunan hanyar magance ta’addan ba da ƙarfin Soji ba. Wannan wauta ce. Tamkar muna ƙarfafar su ne,” in ji shi.

  • Ɗaukar Nauyin Ƴan Ta’addan Da Suka Farmake Mu A Kaduna Aka Yi – El-Rufai
  • Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

El-Rufai ya jaddada cewa wannan tsari ba ya fitowa daga gwamnatin Kaduna kai tsaye, sai dai daga Abuja. A cewarsa, “Ba gwamnatin Kaduna ba ce, manufar gwamnatin ƙasa ce da ONSA yasa gaba, kuma Kaduna na ciki. Jihohi da dama sun nuna rashin amincewa, amma wannan ce manufar yanzu — rungumar ƴan bindiga.”

ADVERTISEMENT

Tsohon gwamnan, wanda ya daɗe yana fafutukar a yi amfani da ƙarfin Soji wajen murƙushe ƴan ta’adda, ya sake jaddada matsayinsa cewa “duk wani tubabben ɗan bindiga shi ne wanda aka kashe. Mu kashe su, mu buga da su, mu kawar da su baki ɗaya, sannan idan akwai kashi biyar cikin ɗari da suke son gyara, sai a taimaka musu. Ba za ka taba yin sulhu da maƙiya daga fuskar rauni ko tsoronsa ba, kuma ba za ka ba su kuɗi su je su sayi muggan makamai ba.”

Ya kuma yi gargaɗi cewa muddin wannan manufar biyan kuɗaɗen da neman sulhu da ƴan bindiga na ci gaba, matsalar rashin tsaro a Arewacin Nijeriya ba za ta gushe ba. El-Rufai ya kuma zargi gwamnatin Kaduna ta yanzu da gazawa wajen kare al’umma, yana mai cewa an riƙa biyan kuɗaɗen fansa masu yawan gaske a asirce. “Ni na yi gwamna shekaru takwas, makarantu uku kacal aka kai wa hari. Wannan gwamnati ta shafe shekaru biyu amma fiye da hakan aka kai wa hari. An biya biliyoyin Naira a matsayin kuɗin fansa. Idan gwamnati ko kowa zai musanta, muna da hujjoji, kuma zamu bayyana su lokacin da ya dace,”in ji shi.

LABARAI MASU NASABA

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

Tarayya
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    NAF Ta Kai Hare-Haren Sama Kan Maboyar Ƴan Ta’adda A Borno
  • Abubakar Sulaiman
    Gwamnati Ta Shirya Gina Gidaje 20,000 Duk Shekara Haɗin Gwuiwar Jamus
  • Abubakar Sulaiman
    Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
  • Abubakar Sulaiman
    Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

MASU ALAKA

inec
Manyan Labarai

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta
Manyan Labarai

Mutum 1 Ya Mutu, 7 Sun Jikkata Yayin Da Ginin Majalisar Dokokin Gombe Ya Rufta

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Manyan Labarai

Duk Da Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Ƴan Nijeriya Na Fama Da Tsadar Man Fetur

July 11, 2026
Next Post
Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara – El-Rufai

Rashin Amincewa Da Tsarin Ƴan Kudancin Kaduna Ya Sa Suka Yi Min Mummunar Fassara - El-Rufai

LABARAI MASU NASABA

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

NDLEA Ta Gargaɗi Masu Sana’ar Keke NAPEP Kan Ta’ammali Da Miyagun Ƙwayoyi

July 12, 2026
inec

2027: INEC Ta Tsawaita Wa’adin Miƙa Sunayen ’Yan Takara

July 12, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina

July 12, 2026
Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

Annalena Baerbock: Kasar Sin Babbar Mai Goyon Bayan Tsarin Mabambantan Bangarori Ce

July 11, 2026
Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Kalubalanci A Tabbatar Da Tsagaita Bude Wuta A Gabas Ta Tsakiya

July 11, 2026
Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

Babban Jami’i: Nazartar Mahangar Xi Jinping Mabudi Ne Na Fahimtar Kasar Sin Ta Zamani

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

Xi Da Kim Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Yarjejeniyar Abota, Hadin Gwiwa Da Taimakon Juna Tsakanin Sin Da DPRK

July 11, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina

July 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.