• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Da Aka Samu Mahajjata Masu Juna Biyu Za Su Fuskanci Hukunci – NAHCON

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
NAHCON

Sakamakon yawaitar samun mata masu juna biyu da suka je kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023 da aka kammala, Hukumar Jindadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta yi barazanar sanya wa Hukumar Alhazai na wasu Jihohi takunkumi, da hukumomin da suka bai wa mahajjata masu ciki damar tafiya zuwa kasa mai tsarji domin aikin Hajji.

Kwamishinan tsare-tsare, bincike, kididdiga da bayar da bayanai da ayyukan dakunan karatu na hukumar, Sheikh Suleiman Momoh ne ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi ga manema labarai a Makkah.

  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar
  • Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

Akalla mata tara ne aka samu masu dauke da juna biyu a lokacin aikin Hajjin bana da aka kammala a tsakanin mata mahajjatan Nijeriya, daga ciki uku sun haihu daya kuma ta yi bari.

Sai dai Sheikh Momoh ya wanke hukumar NAHCON daga duk wani abu da ake zarginta da yi, yana mai cewa jami’an jiha ne ke da alhakin wannan abin kunya kuma za su fuskanci sakamakon abin da suka aikata.

“Idan muka koma Abuja, hukumar za ta binciki hanyoyin ladabtar da jihohin da suka bai wa alhazai masu ciki damar zuwa aikin Hajji.

LABARAI MASU NASABA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

“Za mu duba abin da ya cancanta ga wadannan jihohi kuma mu yanke shawarar matakan ladabtar da su. Muna da hanyoyi na cikin gida kan yadda za mu magance wadannan batutuwa.

Duk kuma irin hukucin da muka yanke, za mu sanar da ‘yan Nijeriya,” in ji Momoh.

Ya shaida wa manema labarai cewa NAHCON ta gudanar da gwaje-gwajen daukar ciki ga dukkan mahajjatan da suka zo ta hanyar gwajin ciki kuma an hana wasu mata biyu daga cikinsu zuwa aikin Hajji biyu wadanda aka tabbatar suna dauke da juna biyun.

Ya ce bisa binciken da aka yi, jami’an kiwon lafiya na hukumar jin dadin alhazai ta jihar sun ja hankalin jami’an jihohin, cewa wasu maniyyatan na da ciki amma sakataren zartarwa ya yi watsi da kiran ya kuma bai wa matan masu ciki damar zuwa aikin Hajjin.

Da yake jaddadawa a cikin bayanansa, ya ce za a gano irin wadannan jihohin tare da sanya musu takunkumi a kan haka, Suleiman ya nanata cewa NAHCON ba za ta bari jihohin su rika gudanar da nasu tsarin kiwon lafiya su kadai ba.

Shugaban tawagar likitocin NAHCON, Dakta Usman Galadima, ya bayyana cewa a cikin mata bakwai masu ciki da aka gano tun farko, daya ta haihu ne ta hanyar tiyata a lokacin da tayin danta ya kai wata bakwai, yanzu ta rasu) yayin da wata mata kuma cikin nata ya zube a sakamakon matsi irin na aikin Hajji.

Ya lissafa jihohin da aka samu mata mahajjatansu sun haihu wadanda mata ne guda bakwai, da suka hada da Sakkoto mutum (2), Katsina mace daya, Yobe mace daya, Adamawa mace daya, Kwara mace daya da kuma Filato mace daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Labarai

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Gwamna Yusuf
Labarai

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
Sabbin Ministoci
Labarai

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

Yanayi Mai Launin Zinare A Kasar Sin

November 5, 2025
Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

Dantsoho Ya Nemi Hadin Kan Kasashen Afrika Wajen Bunkasa Tashoshin Jiragen Ruwa

November 5, 2025
Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

Nazarin Cgtn: Kasashe Masu Tasowa Sun Yi Kira Da A Inganta Tsarin Tafiyar Da Harkokin Duniya

November 5, 2025
Gwamna Yusuf

Malam Triump: Ƙungiyoyin Ɗariƙun Sufaye Sun Maka Gwamnan Kano A Kotu

November 5, 2025
An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

An Rufe Canton Fair Na 138 A Guangzhou

November 5, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisa Ta Nuna Damuwa Kan Rahoton Yiwuwar Asarar Dala Biliyan 300 A Badaƙalar Ɗanyen Mai

November 5, 2025
Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

Firaministan Kasar Sin Ya Gabatar Da Jawabi A Bikin Bude CIIE 

November 5, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Na Tattauna Batun Fara Amfani Da Harshen Hausa A Wurin Koyarwa A Makarantu 

November 5, 2025
Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

Sin Za Ta Gyara Matakan Haraji Kan Kayayyakin Da Ake Shigowa Da Su Daga Amurka

November 5, 2025
Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

November 5, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.