ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Da Aka Samu Mahajjata Masu Juna Biyu Za Su Fuskanci Hukunci – NAHCON

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
NAHCON

Sakamakon yawaitar samun mata masu juna biyu da suka je kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023 da aka kammala, Hukumar Jindadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta yi barazanar sanya wa Hukumar Alhazai na wasu Jihohi takunkumi, da hukumomin da suka bai wa mahajjata masu ciki damar tafiya zuwa kasa mai tsarji domin aikin Hajji.

Kwamishinan tsare-tsare, bincike, kididdiga da bayar da bayanai da ayyukan dakunan karatu na hukumar, Sheikh Suleiman Momoh ne ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi ga manema labarai a Makkah.

  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar
  • Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

Akalla mata tara ne aka samu masu dauke da juna biyu a lokacin aikin Hajjin bana da aka kammala a tsakanin mata mahajjatan Nijeriya, daga ciki uku sun haihu daya kuma ta yi bari.

ADVERTISEMENT

Sai dai Sheikh Momoh ya wanke hukumar NAHCON daga duk wani abu da ake zarginta da yi, yana mai cewa jami’an jiha ne ke da alhakin wannan abin kunya kuma za su fuskanci sakamakon abin da suka aikata.

“Idan muka koma Abuja, hukumar za ta binciki hanyoyin ladabtar da jihohin da suka bai wa alhazai masu ciki damar zuwa aikin Hajji.

LABARAI MASU NASABA

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

“Za mu duba abin da ya cancanta ga wadannan jihohi kuma mu yanke shawarar matakan ladabtar da su. Muna da hanyoyi na cikin gida kan yadda za mu magance wadannan batutuwa.

Duk kuma irin hukucin da muka yanke, za mu sanar da ‘yan Nijeriya,” in ji Momoh.

Ya shaida wa manema labarai cewa NAHCON ta gudanar da gwaje-gwajen daukar ciki ga dukkan mahajjatan da suka zo ta hanyar gwajin ciki kuma an hana wasu mata biyu daga cikinsu zuwa aikin Hajji biyu wadanda aka tabbatar suna dauke da juna biyun.

Ya ce bisa binciken da aka yi, jami’an kiwon lafiya na hukumar jin dadin alhazai ta jihar sun ja hankalin jami’an jihohin, cewa wasu maniyyatan na da ciki amma sakataren zartarwa ya yi watsi da kiran ya kuma bai wa matan masu ciki damar zuwa aikin Hajjin.

Da yake jaddadawa a cikin bayanansa, ya ce za a gano irin wadannan jihohin tare da sanya musu takunkumi a kan haka, Suleiman ya nanata cewa NAHCON ba za ta bari jihohin su rika gudanar da nasu tsarin kiwon lafiya su kadai ba.

Shugaban tawagar likitocin NAHCON, Dakta Usman Galadima, ya bayyana cewa a cikin mata bakwai masu ciki da aka gano tun farko, daya ta haihu ne ta hanyar tiyata a lokacin da tayin danta ya kai wata bakwai, yanzu ta rasu) yayin da wata mata kuma cikin nata ya zube a sakamakon matsi irin na aikin Hajji.

Ya lissafa jihohin da aka samu mata mahajjatansu sun haihu wadanda mata ne guda bakwai, da suka hada da Sakkoto mutum (2), Katsina mace daya, Yobe mace daya, Adamawa mace daya, Kwara mace daya da kuma Filato mace daya.

NAHCON
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
Labarai

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.