ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Da Aka Samu Mahajjata Masu Juna Biyu Za Su Fuskanci Hukunci – NAHCON

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
NAHCON

Sakamakon yawaitar samun mata masu juna biyu da suka je kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023 da aka kammala, Hukumar Jindadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta yi barazanar sanya wa Hukumar Alhazai na wasu Jihohi takunkumi, da hukumomin da suka bai wa mahajjata masu ciki damar tafiya zuwa kasa mai tsarji domin aikin Hajji.

Kwamishinan tsare-tsare, bincike, kididdiga da bayar da bayanai da ayyukan dakunan karatu na hukumar, Sheikh Suleiman Momoh ne ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi ga manema labarai a Makkah.

  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar
  • Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

Akalla mata tara ne aka samu masu dauke da juna biyu a lokacin aikin Hajjin bana da aka kammala a tsakanin mata mahajjatan Nijeriya, daga ciki uku sun haihu daya kuma ta yi bari.

ADVERTISEMENT

Sai dai Sheikh Momoh ya wanke hukumar NAHCON daga duk wani abu da ake zarginta da yi, yana mai cewa jami’an jiha ne ke da alhakin wannan abin kunya kuma za su fuskanci sakamakon abin da suka aikata.

“Idan muka koma Abuja, hukumar za ta binciki hanyoyin ladabtar da jihohin da suka bai wa alhazai masu ciki damar zuwa aikin Hajji.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Za mu duba abin da ya cancanta ga wadannan jihohi kuma mu yanke shawarar matakan ladabtar da su. Muna da hanyoyi na cikin gida kan yadda za mu magance wadannan batutuwa.

Duk kuma irin hukucin da muka yanke, za mu sanar da ‘yan Nijeriya,” in ji Momoh.

Ya shaida wa manema labarai cewa NAHCON ta gudanar da gwaje-gwajen daukar ciki ga dukkan mahajjatan da suka zo ta hanyar gwajin ciki kuma an hana wasu mata biyu daga cikinsu zuwa aikin Hajji biyu wadanda aka tabbatar suna dauke da juna biyun.

Ya ce bisa binciken da aka yi, jami’an kiwon lafiya na hukumar jin dadin alhazai ta jihar sun ja hankalin jami’an jihohin, cewa wasu maniyyatan na da ciki amma sakataren zartarwa ya yi watsi da kiran ya kuma bai wa matan masu ciki damar zuwa aikin Hajjin.

Da yake jaddadawa a cikin bayanansa, ya ce za a gano irin wadannan jihohin tare da sanya musu takunkumi a kan haka, Suleiman ya nanata cewa NAHCON ba za ta bari jihohin su rika gudanar da nasu tsarin kiwon lafiya su kadai ba.

Shugaban tawagar likitocin NAHCON, Dakta Usman Galadima, ya bayyana cewa a cikin mata bakwai masu ciki da aka gano tun farko, daya ta haihu ne ta hanyar tiyata a lokacin da tayin danta ya kai wata bakwai, yanzu ta rasu) yayin da wata mata kuma cikin nata ya zube a sakamakon matsi irin na aikin Hajji.

Ya lissafa jihohin da aka samu mata mahajjatansu sun haihu wadanda mata ne guda bakwai, da suka hada da Sakkoto mutum (2), Katsina mace daya, Yobe mace daya, Adamawa mace daya, Kwara mace daya da kuma Filato mace daya.

NAHCON
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.