ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jihohin Da Aka Samu Mahajjata Masu Juna Biyu Za Su Fuskanci Hukunci – NAHCON

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
NAHCON

Sakamakon yawaitar samun mata masu juna biyu da suka je kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023 da aka kammala, Hukumar Jindadin Alhazai ta Nijeriya (NAHCON) ta yi barazanar sanya wa Hukumar Alhazai na wasu Jihohi takunkumi, da hukumomin da suka bai wa mahajjata masu ciki damar tafiya zuwa kasa mai tsarji domin aikin Hajji.

Kwamishinan tsare-tsare, bincike, kididdiga da bayar da bayanai da ayyukan dakunan karatu na hukumar, Sheikh Suleiman Momoh ne ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi ga manema labarai a Makkah.

  • Yau Kotu Za Ta Yanke Hukunci Kan Karar Da Emefiele Ya Shigar
  • Jakadan Sin A Nijeriya Ya Gana Da Shugaban APC Ta Kasar

Akalla mata tara ne aka samu masu dauke da juna biyu a lokacin aikin Hajjin bana da aka kammala a tsakanin mata mahajjatan Nijeriya, daga ciki uku sun haihu daya kuma ta yi bari.

ADVERTISEMENT

Sai dai Sheikh Momoh ya wanke hukumar NAHCON daga duk wani abu da ake zarginta da yi, yana mai cewa jami’an jiha ne ke da alhakin wannan abin kunya kuma za su fuskanci sakamakon abin da suka aikata.

“Idan muka koma Abuja, hukumar za ta binciki hanyoyin ladabtar da jihohin da suka bai wa alhazai masu ciki damar zuwa aikin Hajji.

LABARAI MASU NASABA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

“Za mu duba abin da ya cancanta ga wadannan jihohi kuma mu yanke shawarar matakan ladabtar da su. Muna da hanyoyi na cikin gida kan yadda za mu magance wadannan batutuwa.

Duk kuma irin hukucin da muka yanke, za mu sanar da ‘yan Nijeriya,” in ji Momoh.

Ya shaida wa manema labarai cewa NAHCON ta gudanar da gwaje-gwajen daukar ciki ga dukkan mahajjatan da suka zo ta hanyar gwajin ciki kuma an hana wasu mata biyu daga cikinsu zuwa aikin Hajji biyu wadanda aka tabbatar suna dauke da juna biyun.

Ya ce bisa binciken da aka yi, jami’an kiwon lafiya na hukumar jin dadin alhazai ta jihar sun ja hankalin jami’an jihohin, cewa wasu maniyyatan na da ciki amma sakataren zartarwa ya yi watsi da kiran ya kuma bai wa matan masu ciki damar zuwa aikin Hajjin.

Da yake jaddadawa a cikin bayanansa, ya ce za a gano irin wadannan jihohin tare da sanya musu takunkumi a kan haka, Suleiman ya nanata cewa NAHCON ba za ta bari jihohin su rika gudanar da nasu tsarin kiwon lafiya su kadai ba.

Shugaban tawagar likitocin NAHCON, Dakta Usman Galadima, ya bayyana cewa a cikin mata bakwai masu ciki da aka gano tun farko, daya ta haihu ne ta hanyar tiyata a lokacin da tayin danta ya kai wata bakwai, yanzu ta rasu) yayin da wata mata kuma cikin nata ya zube a sakamakon matsi irin na aikin Hajji.

Ya lissafa jihohin da aka samu mata mahajjatansu sun haihu wadanda mata ne guda bakwai, da suka hada da Sakkoto mutum (2), Katsina mace daya, Yobe mace daya, Adamawa mace daya, Kwara mace daya da kuma Filato mace daya.

NAHCON
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijar Ta Rattaba Hannu A Kan Dokar Haramta Auren Jinsi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Za Mu Iya Sayar Da Manmu Ba Tare Da Wata Matsala Ba -Iran
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Nijeriya Ta Karbi Ƴan Nijeriya 268 Da Suka Tsero Daga Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Next Post
Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

Gwamnan Sakkwato Ya Kafa Kwamitin Da Zai Binciki Tambuwal

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.