• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sir Sherard Cowper-Coles: Biritaniya Da Sin Suna Amfana Daga Karuwar Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Sir Sherard Cowper-Coles: Biritaniya Da Sin Suna Amfana Daga Karuwar Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin wata hira ta musamman ta kafar bidiyo da ya yi da manema labarai, na kamfanin dillancin labarai na Xinhua na kasar Sin a baya-bayan nan, Sir Sherard Cowper-Coles, shugaban majalisar harkokin kasuwanci tsakanin Sin da Birtaniya, ya ce kasashen Birtaniya da Sin, za su ci gajiyar kud-da-kut a fannin zuba jari da huldar kasuwanci. Ya yi amfani da wani karin magana na Turancin Ingilishi, dake bayyana cewa, “Karuwar ruwa a teku na taimakawa tafiyar jirgin ruwa.” 

Sherard Cowper-Coles ya ce “manyan jiragen ruwa biyu na Biritaniya da Sin, za su yi shawagi da kyau a ruwa mai karuwar wadata”.

  • Cinikayyar Albarkatun Gona Na Kasar Sin Da Kasashen Ketare Ta Karu Da Kaso 6.4 Bisa Dari A Rabin Shekarar Bana 

A kwanan baya, Sherard Cowper-Coles, da sauran wakilan majalisar harkokin kasuwanci na Sin da Birtaniya sun ziyarci wasu biranen kasar Sin, ciki har da Shenzhen, da Shanghai, da Beijing da kuma Guangzhou. Bayan rangadin na su, Cowper-Coles ya bayyana cewa, ya gano cewa, kamfanonin Birtaniya dake kasar Sin, sun fi kyautata zaton samun bunkasuwar kasuwannin kasar Sin.

Ya ce, a shekarar 2022, yawan cinikayyar da ke tsakanin kasashen Birtaniya da Sin ya kai wani sabon matsayi, kuma dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu ta shiga wani sabon mataki. Cowper-Coles ya kara da cewa, sana’o’i da yawa na Birtaniya suna da damar samun ci gaba sosai a kasuwannin kasar Sin, kaza lika kayayyakin da suka hada da motoci, da tufafi, da kifin salmon, na samun karbuwa sosai ga masu sayayya na kasar Sin. A sa’i daya kuma, kasar Birtaniya ita ma na shigo da tarin kayayyaki daga kasar ta Sin.

Da yake magana kan fannonin zuba jari da ake da damar yin hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu, Cowper-Coles ya ce, kasashen Birtaniya da Sin sun dukufa, wajen cimma burin rage gurbata muhalli. Bugu da kari, karuwar bukatun kiwon lafiya na masayan kayan kasar Sin, na samar da damammaki ga kamfanonin Burtaniya a fannonin kiwon lafiya, da kimiyyar rayuwa da dai sauransu. Ya kuma yi maraba da yadda kasar Sin ke ci gaba da inganta bude kofa a fannin harkokin kudi. (Mai fassara: Bilkisu Xin)

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Na Rasa Gane Kan Mijina Tunda Budurwarsa Ta Yi Aure, A Ba Ni Shawara’

Next Post

Kiris Mahaifina Ya Sa A Kama Wanda Ya Fara Sa Ni Fim Amma… – Maryam Kimono

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

16 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

18 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

18 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

22 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

24 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

1 day ago
Next Post
Kiris Mahaifina Ya Sa A Kama Wanda Ya Fara Sa Ni Fim Amma… – Maryam Kimono

Kiris Mahaifina Ya Sa A Kama Wanda Ya Fara Sa Ni Fim Amma… - Maryam Kimono

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.