• English
  • Business News
Thursday, August 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Mai: Babu Shirin Karin Kudin Kiran Waya – NCC

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Cire Tallafin Mai: Babu Shirin Karin Kudin Kiran Waya – NCC
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da harkokin sadarwa ta Nijeriya (NCC) ta nanata cewa babu wani shirin kara kudin kiran wayar tarho sakamakon cire tallafin Mai.

Babban mataimakin shugaban hukumar NCC, Farfesa Umar Garba Danbatta ne ya bada wannan tabbacin a karshen mako yayin da yake amsar lambar yabon Titans of Tech (ToT) a jihar Legas.

  • Rundunar ‘Yan Sanda Sun Cafke Dan Yahoo Da Ya Kware Kan Cutar ‘Yan Kasar Hungary A Nijeriya

Dambatta na cewa: “NCC ta fada cewa ba ta shirya kara kudin kiran waya a yanzu sakamakon cire tallafin Mai ba. Irin wannan matakin ya rage ga dukkanin kamfanonin sadarwa su duba abun da za su yanke. Mun tattauna sosai da dukkanin kamfanonin. Don haka wannan ya rage musu su cimma matsaya. Muna tafiyar da aiki da shigo da kowa cikin lamura a NCC. Ba mu yi magana kan karin kudin wayar tarho ba ya zuwa yanzu.”

Dambatta wanda ya samu wakilcin shugaban hukumar na shiyyar Legas, Mr Yomi Arowosafe, wanda ya amshi lambar yabon gwarzon ‘Pan African Telecoms Operator’ na shekara, yayin da kuma kakakin hukumar Mr Reuben Muoka ya amshi lambar yabon gwarzon jami’in sadarwa na shekara.

Dambatta ya gode wa kamfanin da suka shirya lambar yabon tare da zakule shi hadi da karrama shi. Ya nuna hakan a matsayin matakin da zai kara masa azama a fagen aiki.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

Tun da farko da yake jawabi a wajen taron, tsohon gwamnan jihar Legas, Mr Femi Pedro, ya bukaci masu ruwa da tsaki da su ke bayar da fifiko da muhimmanci ga darussan kimiyya, fasaha, injiniyanci da lissafi (STEM) tun daga matakin firemare har zuwa babban matakin karatu.

Kazalika, ya ce, lokaci ya yi da za a karfafi matasa kan hanyoyin dogaro da kai, kirkire-kirkire ta hanyar amfani da fasahar zamani, “Wasu matasa da dama suna ta korafin babu aikin yi, alhali ga hanyoyin da za a iya samun abun yi ta kimiyya ta hanyar kirkire-kirkire.

“Babu bukatar wani ya zauna babu aikin yi a duniyar yau.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Muhimman Abubuwan Da Takardar Karin Kudin Makarantar Sakandaren Gwamnatin Tarayya Ta Kunsa

Next Post

Kamfanin Twitter Ya Maye Gurbin Tambarin Tsuntsu Da X

Related

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

19 minutes ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

33 minutes ago
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000
Manyan Labarai

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

2 hours ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 hours ago
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano
Manyan Labarai

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

5 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

6 hours ago
Next Post
Kamfanin Twitter Ya Maye Gurbin Tambarin Tsuntsu Da X

Kamfanin Twitter Ya Maye Gurbin Tambarin Tsuntsu Da X

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

August 28, 2025
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

August 28, 2025
Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

Ƴansandan Libya Sun Kama Ƴan Nijeriya Biyu Kan Zargin Fashi

August 28, 2025
Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

Hukumar Shige Da Fice Ta Ƙara Kuɗin Fasfo Zuwa N100,000, N200,000

August 28, 2025
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

August 28, 2025
Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

Ba Zan Nemi Kujerar Siyasa A 2027 Ba — El-Rufai

August 28, 2025
An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

August 28, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

August 28, 2025
Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

August 28, 2025
ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027 – Amaechi

August 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.