• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin JKS Sun Gabatar Da Taswirar Abubuwan Dake Kan Gaba Wajen Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watanni 6 Na Karshen Bana

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin JKS Sun Gabatar Da Taswirar Abubuwan Dake Kan Gaba Wajen Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watanni 6 Na Karshen Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ta gudanar da taro a Litinin din nan, da nufin nazarin halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, tare da tsara dabarun raya ayyukan bunkasa tattalin arzikin kasar a watanni 6 na karshen shekarar bana. Taron ya gudana ne karkashin jagorancin shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Xi Jinping.

Mahalarta taron dai sun yi kira da a aiwatar da ka’idojin raya sassan tattalin arziki bisa dacewa da karsashi, da gaggauta kawar da dokokin da ka iya haifar da koma baya, da kirkiro karin manufofi da ka iya taimakawa cimma burin da aka sanya gaba.

  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Na Daliban Jami’o’i

Kaza lika, mahalartan sun yi imanin cewa, ya zama doke a nacewa aiwatar da matakai mafiya dacewa, da manufofin kudi masu inganci, da aiwatar da su bisa gaskiya. Kana a fadada, da kyautata, da inganta, da kuma tabbatar da an aiwatar da manufofin haraji, da na rangwamen biyan kudade, kana a aiwatar da manufofin kudi masu tsari don cimma nasara.

Har ila yau, taron ya amince a karfafa goyon baya, ga fannonin kimiyya da kirkire-kirkiren fasaha, da fannin tattalin arziki na zahiri, da raya kanana da matsakaitan kamfanoni.

Kafin hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin a shirya wannan taron, kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta Sin ya shirya wani taron kara wa juna sani domin karbar shawarwari daga wadanda ba ’yan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ba, da nufin jin ra’ayoyin da suka shafi halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, da ayyukan da ake aiwatarwa na raya tattalin arzikin kasar, a watanni 6 na karshen shekarar nan.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, shi ne ya jagoranci zaman taron, tare da gabatar da muhimmin jawabi a ranar Juma’ar da ta gabata.

Cikin jawabin da ya gabatar, Xi ya ce idan ana son gudanar da aikin raya tattalin arziki cikin watanni 6 na karshen shekarar nan yadda ya kamata, ya wajaba a yi aiki da manyan ka’idojin cimma nasarori, tare da wanzar da daidaito.

Ya ce kamata ya yi a kara azama wajen aiwatar da dukkanin sabbin dabarun bunkasuwa ta dukkanin bangarori, da ingiza gina sabon salon ci gaba, da zurfafa cikakkun sauye-sauye da kara bude kofa, da zurfafa amfani da dokoki masu nasaba, da fadada bukatun cikin gida, da bunkasa kwarin gwiwa da kare hadurra.

Daga nan sai shugaba Xi ya jaddada muhimmancin kara azamar ci gaba da kyautata nasarar bunkasar tattalin arziki, da karfafa tasirin karfin dake ingiza nasarar hakan, da fatan al’ummun kasa, kana a ci gaba da dakile asara da boyayyun hadurra, a kuma daga inganci, da fadada nasarorin da ake samu daga tattalin arzikin kasar Sin. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

Next Post

Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

6 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

6 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

8 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

11 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

12 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

13 hours ago
Next Post
Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.