• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin JKS Sun Gabatar Da Taswirar Abubuwan Dake Kan Gaba Wajen Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watanni 6 Na Karshen Bana

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Shugabannin JKS Sun Gabatar Da Taswirar Abubuwan Dake Kan Gaba Wajen Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watanni 6 Na Karshen Bana
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ta gudanar da taro a Litinin din nan, da nufin nazarin halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, tare da tsara dabarun raya ayyukan bunkasa tattalin arzikin kasar a watanni 6 na karshen shekarar bana. Taron ya gudana ne karkashin jagorancin shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Xi Jinping.

Mahalarta taron dai sun yi kira da a aiwatar da ka’idojin raya sassan tattalin arziki bisa dacewa da karsashi, da gaggauta kawar da dokokin da ka iya haifar da koma baya, da kirkiro karin manufofi da ka iya taimakawa cimma burin da aka sanya gaba.

  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Na Daliban Jami’o’i

Kaza lika, mahalartan sun yi imanin cewa, ya zama doke a nacewa aiwatar da matakai mafiya dacewa, da manufofin kudi masu inganci, da aiwatar da su bisa gaskiya. Kana a fadada, da kyautata, da inganta, da kuma tabbatar da an aiwatar da manufofin haraji, da na rangwamen biyan kudade, kana a aiwatar da manufofin kudi masu tsari don cimma nasara.

Har ila yau, taron ya amince a karfafa goyon baya, ga fannonin kimiyya da kirkire-kirkiren fasaha, da fannin tattalin arziki na zahiri, da raya kanana da matsakaitan kamfanoni.

Kafin hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin a shirya wannan taron, kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta Sin ya shirya wani taron kara wa juna sani domin karbar shawarwari daga wadanda ba ’yan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ba, da nufin jin ra’ayoyin da suka shafi halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, da ayyukan da ake aiwatarwa na raya tattalin arzikin kasar, a watanni 6 na karshen shekarar nan.

Labarai Masu Nasaba

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, shi ne ya jagoranci zaman taron, tare da gabatar da muhimmin jawabi a ranar Juma’ar da ta gabata.

Cikin jawabin da ya gabatar, Xi ya ce idan ana son gudanar da aikin raya tattalin arziki cikin watanni 6 na karshen shekarar nan yadda ya kamata, ya wajaba a yi aiki da manyan ka’idojin cimma nasarori, tare da wanzar da daidaito.

Ya ce kamata ya yi a kara azama wajen aiwatar da dukkanin sabbin dabarun bunkasuwa ta dukkanin bangarori, da ingiza gina sabon salon ci gaba, da zurfafa cikakkun sauye-sauye da kara bude kofa, da zurfafa amfani da dokoki masu nasaba, da fadada bukatun cikin gida, da bunkasa kwarin gwiwa da kare hadurra.

Daga nan sai shugaba Xi ya jaddada muhimmancin kara azamar ci gaba da kyautata nasarar bunkasar tattalin arziki, da karfafa tasirin karfin dake ingiza nasarar hakan, da fatan al’ummun kasa, kana a ci gaba da dakile asara da boyayyun hadurra, a kuma daga inganci, da fadada nasarorin da ake samu daga tattalin arzikin kasar Sin. (Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Mbappe Ya Samu Tayin Fam Miliyan 300 Daga Al Hilal Ta Saudiya

Next Post

Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

Related

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

32 minutes ago
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

18 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

19 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

20 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

21 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

22 hours ago
Next Post
Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

LABARAI MASU NASABA

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

September 13, 2025
An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

An Shirya Haɗin Gwiwa Da Hukumomi Don Magance Matsalar Ambaliyar Ruwa

September 13, 2025
Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

Majalisar Tarayya Ta Magantu Kan Gawar Da Aka Samu A Harabarta

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Sabon Sharaɗi Na Buɗe Asusun Banki

September 13, 2025
PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

PDP Ta Dage Kan Gudanar Da Taronta Duk Da Sabbin Sharuɗɗan Da Ɓangaren Wike Ya Gindaya

September 13, 2025
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.