ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin JKS Sun Gabatar Da Taswirar Abubuwan Dake Kan Gaba Wajen Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watanni 6 Na Karshen Bana

by CMG Hausa
3 years ago
JKS

Hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ta gudanar da taro a Litinin din nan, da nufin nazarin halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, tare da tsara dabarun raya ayyukan bunkasa tattalin arzikin kasar a watanni 6 na karshen shekarar bana. Taron ya gudana ne karkashin jagorancin shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Xi Jinping.

Mahalarta taron dai sun yi kira da a aiwatar da ka’idojin raya sassan tattalin arziki bisa dacewa da karsashi, da gaggauta kawar da dokokin da ka iya haifar da koma baya, da kirkiro karin manufofi da ka iya taimakawa cimma burin da aka sanya gaba.

  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Na Daliban Jami’o’i

Kaza lika, mahalartan sun yi imanin cewa, ya zama doke a nacewa aiwatar da matakai mafiya dacewa, da manufofin kudi masu inganci, da aiwatar da su bisa gaskiya. Kana a fadada, da kyautata, da inganta, da kuma tabbatar da an aiwatar da manufofin haraji, da na rangwamen biyan kudade, kana a aiwatar da manufofin kudi masu tsari don cimma nasara.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, taron ya amince a karfafa goyon baya, ga fannonin kimiyya da kirkire-kirkiren fasaha, da fannin tattalin arziki na zahiri, da raya kanana da matsakaitan kamfanoni.

Kafin hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin a shirya wannan taron, kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta Sin ya shirya wani taron kara wa juna sani domin karbar shawarwari daga wadanda ba ’yan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ba, da nufin jin ra’ayoyin da suka shafi halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, da ayyukan da ake aiwatarwa na raya tattalin arzikin kasar, a watanni 6 na karshen shekarar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, shi ne ya jagoranci zaman taron, tare da gabatar da muhimmin jawabi a ranar Juma’ar da ta gabata.

Cikin jawabin da ya gabatar, Xi ya ce idan ana son gudanar da aikin raya tattalin arziki cikin watanni 6 na karshen shekarar nan yadda ya kamata, ya wajaba a yi aiki da manyan ka’idojin cimma nasarori, tare da wanzar da daidaito.

Ya ce kamata ya yi a kara azama wajen aiwatar da dukkanin sabbin dabarun bunkasuwa ta dukkanin bangarori, da ingiza gina sabon salon ci gaba, da zurfafa cikakkun sauye-sauye da kara bude kofa, da zurfafa amfani da dokoki masu nasaba, da fadada bukatun cikin gida, da bunkasa kwarin gwiwa da kare hadurra.

Daga nan sai shugaba Xi ya jaddada muhimmancin kara azamar ci gaba da kyautata nasarar bunkasar tattalin arziki, da karfafa tasirin karfin dake ingiza nasarar hakan, da fatan al’ummun kasa, kana a ci gaba da dakile asara da boyayyun hadurra, a kuma daga inganci, da fadada nasarorin da ake samu daga tattalin arzikin kasar Sin. (Saminu Alhassan)

JKS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026
Daga Birnin Sin

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Next Post
Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.