ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabannin JKS Sun Gabatar Da Taswirar Abubuwan Dake Kan Gaba Wajen Raya Tattalin Arzikin Kasar Sin A Watanni 6 Na Karshen Bana

by CMG Hausa
3 years ago
JKS

Hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin, ta gudanar da taro a Litinin din nan, da nufin nazarin halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, tare da tsara dabarun raya ayyukan bunkasa tattalin arzikin kasar a watanni 6 na karshen shekarar bana. Taron ya gudana ne karkashin jagorancin shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin jam’iyyar Xi Jinping.

Mahalarta taron dai sun yi kira da a aiwatar da ka’idojin raya sassan tattalin arziki bisa dacewa da karsashi, da gaggauta kawar da dokokin da ka iya haifar da koma baya, da kirkiro karin manufofi da ka iya taimakawa cimma burin da aka sanya gaba.

  • Xi Jinping Zai Halarci Bikin Bude Gasar Wasannin Motsa Jiki Na Daliban Jami’o’i

Kaza lika, mahalartan sun yi imanin cewa, ya zama doke a nacewa aiwatar da matakai mafiya dacewa, da manufofin kudi masu inganci, da aiwatar da su bisa gaskiya. Kana a fadada, da kyautata, da inganta, da kuma tabbatar da an aiwatar da manufofin haraji, da na rangwamen biyan kudade, kana a aiwatar da manufofin kudi masu tsari don cimma nasara.

ADVERTISEMENT

Har ila yau, taron ya amince a karfafa goyon baya, ga fannonin kimiyya da kirkire-kirkiren fasaha, da fannin tattalin arziki na zahiri, da raya kanana da matsakaitan kamfanoni.

Kafin hukumar siyasa ta kwamitin kolin jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin a shirya wannan taron, kwamitin kolin Jam’iyyar Kwaminis ta Sin ya shirya wani taron kara wa juna sani domin karbar shawarwari daga wadanda ba ’yan jam’iyyar kwaminis ta kasar Sin ba, da nufin jin ra’ayoyin da suka shafi halin da tattalin arzikin kasar Sin ke ciki, da ayyukan da ake aiwatarwa na raya tattalin arzikin kasar, a watanni 6 na karshen shekarar nan.

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Shugaban kasar Sin, kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS Xi Jinping, shi ne ya jagoranci zaman taron, tare da gabatar da muhimmin jawabi a ranar Juma’ar da ta gabata.

Cikin jawabin da ya gabatar, Xi ya ce idan ana son gudanar da aikin raya tattalin arziki cikin watanni 6 na karshen shekarar nan yadda ya kamata, ya wajaba a yi aiki da manyan ka’idojin cimma nasarori, tare da wanzar da daidaito.

Ya ce kamata ya yi a kara azama wajen aiwatar da dukkanin sabbin dabarun bunkasuwa ta dukkanin bangarori, da ingiza gina sabon salon ci gaba, da zurfafa cikakkun sauye-sauye da kara bude kofa, da zurfafa amfani da dokoki masu nasaba, da fadada bukatun cikin gida, da bunkasa kwarin gwiwa da kare hadurra.

Daga nan sai shugaba Xi ya jaddada muhimmancin kara azamar ci gaba da kyautata nasarar bunkasar tattalin arziki, da karfafa tasirin karfin dake ingiza nasarar hakan, da fatan al’ummun kasa, kana a ci gaba da dakile asara da boyayyun hadurra, a kuma daga inganci, da fadada nasarorin da ake samu daga tattalin arzikin kasar Sin. (Saminu Alhassan)

JKS
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna
Daga Birnin Sin

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba
Daga Birnin Sin

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa
Daga Birnin Sin

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Next Post
Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

Sharhi: Mu Rungumi Nasarar Sin Kar Mu Tsargu

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.