• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotun Birtaniya Ta Umarci Lauyan Ibori Ya Biya Tarar £28m

by Abubakar Abba
2 years ago
Birtaniya

Wata kotu a Birtaniya, ta umarci Bhadresh Gohil, lauyan tsohon gwamnan jihar Delta, James Ibori da ya biya tarar Fam miliyan 28 bisa taimaka wa da ya yi na boye kudaden da ya samu ta haramtacciyar hanya.

Gohil wanda dan kasar Indiya ne, kotun ta yanke masa hukuncin dauri a 2010 kan tukume-tuhume 13 na yin safarar kudade ta haramtacciyar hanya da da kuma aikata sauran laifukan da ke da nasaba da taimakawa Ibori na boye haramtattun kudade.

  • NLC Ta Bai Wa Tinubu Kwanaki 7 Don Dawo Da Tallafin Mai, Ko Ta Shiga Yajin Aiki 
  • Likitoci Masu Sanin Makamar Aiki Sun Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-Ta-Gani

Ibori, ya shugabanci jihar Delta ne, daga shekarar 1999 zuwa shekarar 2007.

Kazalika, kotun a zamanta na jiya Litinin ta umarci Gohil da ya biya tarar sama da Fam miliyan 28, kuma zai kara fuskantar wani daurin na shekara shida.

Kafar yada labarai ta Reuters, a jiya Litinin ta kafa hujjarta ne da sanarwar da ta samu daga ofishin yanke hukunci na CPS na Birtaniya.

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

Kotun dai, ta yanke Gohil hukuncin zaman gidan yari na shekaru 10 ne a 2010, wanda ya yi zaman rabin hukuncin, a gidan yari.

Kotun ta dauki wannan matakin ne, bayan ta yanke wa Ibori hukuncin dauri kan safarar haramtattun miliyoyin kudade a Birtaniya da wasu wuraren, inda kuma kotun a ranar Juma’ar da ta wuce, ta umarce shi da ya biya tarar Fam miliyan 101.5 wanda ya yi daidai da dala miliyan 130, ko kuma ya kara fuskantar wani hukuncin dauri na shekaru takwas.

Sai dai, a ranar Juma’ar, Ibori ya lashi takobin daukaka kara kan wannan hukunci, wanda aka yanke masa.

Bisa ga bayanan da kafar yada labarai ta Reuters samu daga ofishin CPS da ke a Birtaniya a karkashin dokar samun bayanai, bayan da Birtaniya ta karfafa dokar aikata manyan laifuka a shekarar 2002, laifin kwace kayan Ibori shi ne mafi girma na biyu, inda kuma na lauyansa Gohil ya kasance mafi girma na biyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati
Labarai

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba
Labarai

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Next Post
Jami’an Tsaro Sun Tsare Shugaban Nijar Kan Fargabar Yunkurin Juyin Mulki

Jami'an Tsaro Sun Tsare Shugaban Nijar Kan Fargabar Yunkurin Juyin Mulki

LABARAI MASU NASABA

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

Adadin Biyan Kudade Ta Intanet Yayin Hutun Bikin Kafuwar Jamhuriyar Jama’ar Sin Ya Kai Yuan Tiriliyan 13.26

October 9, 2025
SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.