• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Zauren Malaman Nijeriya ya gargadi shugaban Nijeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS, Bola Ahmed Tinubu dangane da yunkurin daukar matakin soji a kan Jamhuriyar Nijar, biyo bayan hambarar da gwamnatin farar hula da sojoji suka yi.

Malaman sun ce matakin ba zai haifar da sakamako mai kyau ga kasashen biyu ba.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6
  • Nijar Ta Yanke Hulda Tsakaninta Da Nijeriya

Malaman sun nemi kowane bangare da ya dauki matakin salama cikin yanayin diflomasiyya domin tallafawa Jamhuriyar Nijar da mutanenta.

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da kungiyar ta yi, inda shugabanta Aminu Inuwa Muhammad, da sakatarenta Injiniya Basheer Adamu Aliyu da suka cimma a ranar Juma’a.

Sun yi fatan cewa majalisar dokokin Nijeriya ba za ta amince wajen bari a shiga cikin wannan rigimar ba wadda ka iya zama yaki.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

Kazalika, malaman sun jawo hankalin malamai a dukkanin matakai da su dukufa wajen fadakarwa da jan hankali kan illar janyo fada tsakanin makwabta tare da tabbatar da dorewar alakar tsakanin Nijeriya da Nijar.

“Yana da kyau gwamnatin Nijeriya ta sake yin duba kan kokarin da ta ke yi, sannan kuma ga barazanar tsaro ta ko ina, wadanda su ke ta tatse ‘yar lalitar kasar, kada a afka mu cikin wani rikici da za mu iya kaucewa, kawai don mu farantawa wasu kasashen duniya a siyasance.”

Malaman da suka sanya hannu kan takardar a yayin zaman sun kai 25 daga sassa daban-daban na kasar nan, inda suka yi fatan cewa barazanar da ake gani a zahirance ba zai kai ga janyo barakar zaman lafiya a tsakanin Nijeriya da Nijar ba.

Zauren ya jadadda goyon bayan matakan diflomasiyya da a ka fara dauka ta hanyar aikewa da wakilai domin zama da jagororin sojin juyin mulkin Nijar don tattaunawa cikin salama.

“Juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar da ma duk wadanda a ka yi a sauran kasashen yankin SAHEL abun takaici ne, kuma ya cancanci duk masu ra’ayin dimokuradiyya su yi tir da shi da ma duk masu neman zaman lafiya a duniya.

“Duk da cewa mutane da dama na fifita dimokradiyya da tsare-tsarenta, amma hanyar samar da shugabanci na gari, abu ne da ya kebanci mutanen kowace kasa su kadai. Don haka damar mutanen Jamhuriyyar Nijar ce su bi duk hanyoyin da su ka ga sun dace domin dawo da dimokradiyya a kasarsu, idan sun ga hakan ya dace; kuma duk wani kokarin da wani zai yi, a ko ina yake, matukar ba mutanen Nijar ba, abu ne da zai yi karan tsaye ga dimokradiyya da sunan samar da dimokradiyya.”

Malaman sun ce wa’adin kwanaki bakwai da ECOWAS ta bai wa jagororin sojin kasar ya ci karo da tanade-tanaden dimokradiyya kuma shisshigi ne ga ‘yancin gudanar da kasa mai cin gashin kanta.

Sanarwar ta ce, kaso mafi rinjaye na al’ummar Nijeriya ba su goyon bayan yakar Nijar wadda ke da kyakkyawar alaka.

“Abin da ya fi wannan hatsari kuma, shiga wannan yaki zai jawo a mayar da wanan yankin namu wani zakaran gwajin dafi da za a yi amfani da shi wajen wasa kwanji da gwajin makamai, daga kasashen waje da ke da muggan manofofi ga wannan yankin.

“Kuma amfani da karfin soji zai haifar da wuce gona da iri game da babban aikin ECOWAS na samar da tsaro da kariya daga kasashen waje, ya ba da dama ga wasu su sa muke fada da juna.”

Malaman da suka sanya hannu a sanarwar sun hada da Malam Aminu Inuwa Muhammad, Jagora, Kano; Prof. Mansur Ibrahim Sokoto mni, Mamba, Sokoto; Dr. Bashir Aliyu Umar, Mamba, Kano 04 Dr. Sa’id Ahmad Dukawa, Mamba, Kano; Dr. Abubakar Muhammad Sani B/Kudu, Mamba, Jigawa; Dr. Khalid Abubakar Aliyu, Mamba, Kaduna; Prof. Muhammad Babangida Muhammad, Mamba, Kano; Prof. Salisu Shehu, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Bello Dogarawa, Mamba, Kaduna; da kuma Mal Ahmad Bello Abu Maimounah, Mamba, Katsina.

Sauran su ne: Dr. Muhammad Alhaji Abubakar, Mamba, Borno; Malam Muhammad Lawal Maidoki, Sadaukin Sokoto, Mamba, Sokoto; Malam Aminu Aliyu Gusau, Modibbon Gusau, Mamba, Zamfara; Mal Shehu Muhammad Maishanu, Mamba, Zamfara; Prof Muhammad Amin Al-Amin, Mamba, Katsina; Barrister Ibrahim Muhammad Attahir, Mamba, Gombe; Dr. Salisu Ismail, Mamba, Jigawa

Dr. Abubakar Saidu, Mamba, Gombe; Engr. Ahmad Y. M. Jumba, Mamba, Bauchi; Amir Abdullahi Abubakar Lamido, Mamba, Gombe.

Kazalika akwai Dr. Ibrahim Adam Omar Disina, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Murtala, Mamba, Kano; Prof. Usman M. Shuaibu Zunnurain, Mamba, Katsina; Malam Ibrahim Ado-Kurawa, Mamba, Kano da Engr. Basheer Adamu Aliyu, Sakatare, Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASJuyin MulkiMalamaiNijarNijeriyaSojojiUlamaYaki
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6

Next Post

Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

Related

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

11 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

13 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

16 hours ago
Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu
Rahotonni

Yadda Masu Bukata Ta Musamman Suka Rungumi Sabbin Dabarun Noma Domin Ciyar Da Kansu

17 hours ago
Next Post
Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Malamai

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (6)

Dalilan Da Suka Sa Cinikin Bayi Bai Yi Nasara A Arewacin Nijeriya Ba

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.