ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Malamai Sun Gargadi Tinubu Kan Daukar Matakin Soji A Kan Nijar

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Malamai

Zauren Malaman Nijeriya ya gargadi shugaban Nijeriya kuma shugaban kungiyar ECOWAS, Bola Ahmed Tinubu dangane da yunkurin daukar matakin soji a kan Jamhuriyar Nijar, biyo bayan hambarar da gwamnatin farar hula da sojoji suka yi.

Malaman sun ce matakin ba zai haifar da sakamako mai kyau ga kasashen biyu ba.

  • An Gurfanar Da Wani Mutum Da Ya Kashe Kaninsa Dan Shekara 6
  • Nijar Ta Yanke Hulda Tsakaninta Da Nijeriya

Malaman sun nemi kowane bangare da ya dauki matakin salama cikin yanayin diflomasiyya domin tallafawa Jamhuriyar Nijar da mutanenta.

ADVERTISEMENT

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da kungiyar ta yi, inda shugabanta Aminu Inuwa Muhammad, da sakatarenta Injiniya Basheer Adamu Aliyu da suka cimma a ranar Juma’a.

Sun yi fatan cewa majalisar dokokin Nijeriya ba za ta amince wajen bari a shiga cikin wannan rigimar ba wadda ka iya zama yaki.

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Kazalika, malaman sun jawo hankalin malamai a dukkanin matakai da su dukufa wajen fadakarwa da jan hankali kan illar janyo fada tsakanin makwabta tare da tabbatar da dorewar alakar tsakanin Nijeriya da Nijar.

“Yana da kyau gwamnatin Nijeriya ta sake yin duba kan kokarin da ta ke yi, sannan kuma ga barazanar tsaro ta ko ina, wadanda su ke ta tatse ‘yar lalitar kasar, kada a afka mu cikin wani rikici da za mu iya kaucewa, kawai don mu farantawa wasu kasashen duniya a siyasance.”

Malaman da suka sanya hannu kan takardar a yayin zaman sun kai 25 daga sassa daban-daban na kasar nan, inda suka yi fatan cewa barazanar da ake gani a zahirance ba zai kai ga janyo barakar zaman lafiya a tsakanin Nijeriya da Nijar ba.

Zauren ya jadadda goyon bayan matakan diflomasiyya da a ka fara dauka ta hanyar aikewa da wakilai domin zama da jagororin sojin juyin mulkin Nijar don tattaunawa cikin salama.

“Juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar da ma duk wadanda a ka yi a sauran kasashen yankin SAHEL abun takaici ne, kuma ya cancanci duk masu ra’ayin dimokuradiyya su yi tir da shi da ma duk masu neman zaman lafiya a duniya.

“Duk da cewa mutane da dama na fifita dimokradiyya da tsare-tsarenta, amma hanyar samar da shugabanci na gari, abu ne da ya kebanci mutanen kowace kasa su kadai. Don haka damar mutanen Jamhuriyyar Nijar ce su bi duk hanyoyin da su ka ga sun dace domin dawo da dimokradiyya a kasarsu, idan sun ga hakan ya dace; kuma duk wani kokarin da wani zai yi, a ko ina yake, matukar ba mutanen Nijar ba, abu ne da zai yi karan tsaye ga dimokradiyya da sunan samar da dimokradiyya.”

Malaman sun ce wa’adin kwanaki bakwai da ECOWAS ta bai wa jagororin sojin kasar ya ci karo da tanade-tanaden dimokradiyya kuma shisshigi ne ga ‘yancin gudanar da kasa mai cin gashin kanta.

Sanarwar ta ce, kaso mafi rinjaye na al’ummar Nijeriya ba su goyon bayan yakar Nijar wadda ke da kyakkyawar alaka.

“Abin da ya fi wannan hatsari kuma, shiga wannan yaki zai jawo a mayar da wanan yankin namu wani zakaran gwajin dafi da za a yi amfani da shi wajen wasa kwanji da gwajin makamai, daga kasashen waje da ke da muggan manofofi ga wannan yankin.

“Kuma amfani da karfin soji zai haifar da wuce gona da iri game da babban aikin ECOWAS na samar da tsaro da kariya daga kasashen waje, ya ba da dama ga wasu su sa muke fada da juna.”

Malaman da suka sanya hannu a sanarwar sun hada da Malam Aminu Inuwa Muhammad, Jagora, Kano; Prof. Mansur Ibrahim Sokoto mni, Mamba, Sokoto; Dr. Bashir Aliyu Umar, Mamba, Kano 04 Dr. Sa’id Ahmad Dukawa, Mamba, Kano; Dr. Abubakar Muhammad Sani B/Kudu, Mamba, Jigawa; Dr. Khalid Abubakar Aliyu, Mamba, Kaduna; Prof. Muhammad Babangida Muhammad, Mamba, Kano; Prof. Salisu Shehu, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Bello Dogarawa, Mamba, Kaduna; da kuma Mal Ahmad Bello Abu Maimounah, Mamba, Katsina.

Sauran su ne: Dr. Muhammad Alhaji Abubakar, Mamba, Borno; Malam Muhammad Lawal Maidoki, Sadaukin Sokoto, Mamba, Sokoto; Malam Aminu Aliyu Gusau, Modibbon Gusau, Mamba, Zamfara; Mal Shehu Muhammad Maishanu, Mamba, Zamfara; Prof Muhammad Amin Al-Amin, Mamba, Katsina; Barrister Ibrahim Muhammad Attahir, Mamba, Gombe; Dr. Salisu Ismail, Mamba, Jigawa

Dr. Abubakar Saidu, Mamba, Gombe; Engr. Ahmad Y. M. Jumba, Mamba, Bauchi; Amir Abdullahi Abubakar Lamido, Mamba, Gombe.

Kazalika akwai Dr. Ibrahim Adam Omar Disina, Mamba, Bauchi; Prof. Ahmad Murtala, Mamba, Kano; Prof. Usman M. Shuaibu Zunnurain, Mamba, Katsina; Malam Ibrahim Ado-Kurawa, Mamba, Kano da Engr. Basheer Adamu Aliyu, Sakatare, Kano.

Malamai
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Next Post
Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

Na Fi So Na Fito A Masifaffiya -Amina Miloniya

LABARAI MASU NASABA

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026
Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.