• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Gargadi Tinubu Kan Shirin Yakar Nijar

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Gargadi  Tinubu Kan Shirin Yakar Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da wa’adin da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta bai wa gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar, ya cika, fitaccen malamin Addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi kira ga shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya shiga yaki da kasar da ke makwabtaka da Nijeriya.

Shahararren malamin, wanda shi ne shugaban darikar Tijjaniya a Nijeriya, ya kuma bukaci majalisar dokokin kasar nan da kada ta amince da bukatar da shugaban kasar ya gabatar mata kan yakar Nijar.

  • AU, UN Da ECOWAS Sun Garzaya Nijar Don Tattaunawa Da Sojin Juyin Mulki
  • Kwatsam Ta Zayyana Ƙa’idoji Kafin Fara Shigo Da Kayayyaki Daga Iyakoki

A cewar dattijon malamin, maimakon su shiga yaki da kasar, kamata ya yi shugaba Tinubu da sauran shugabannin ECOWAS su tattauna da gwamnatin mulkin sojan Nijar da ta hambarar da shugaba Mohammed Bazoum.

Sheikh Bauchi ya bayyana haka ne a Bauchi a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida, inda ya kara da cewa Nijeriya da Jamhuriyar Nijar na da dadaddiyar alakar da ke bukatar kara karfafa ta.

“’Yan Nijeriya da Nijar sun dade a tare. Don haka akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tsunduma cikin harkokin diflomasiyya da nufin karfafa kyakkyawar alakar bunkasar tattalin arziki da ci gaban kasashen Afirka ta Yamma,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

A cewar Shehin malamin, ya yi gargadin cewa, “yana da kyau a samar da wani kuduri na aminci don kaucewa zubar da jinin wadanda ba su ji ba ba su gani ba. ”

Daga nan sai ya bukaci sauran shugabannin Afirka ta Yamma da sauran masu ruwa da tsaki da su rungumi tattaunawa ta diflomasiya.

“Muna kira ga Shugaba Tinubu; Muna kuma kira ga Majalisar Dokoki ta kasa da dukkan shugabannin ECOWAS da masu ruwa da tsaki da kada su shiga da Nijar.

“Wannan kudirin ne na ceto rayukan wadanda ba su ji ba ba su gani ba, da kuma ceto mutane daga shiga cikin kuncin rayuwa,” in ji Sheikh Dahiru Bauchi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASJuyin MulkiNijarSheikh Dahiru BauchiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

AU, UN Da ECOWAS Sun Garzaya Nijar Don Tattaunawa Da Sojin Juyin Mulki

Next Post

Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

Related

‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

1 hour ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

2 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

4 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

5 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

8 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

9 hours ago
Next Post
Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

LABARAI MASU NASABA

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.