• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Gargadi Tinubu Kan Shirin Yakar Nijar

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Gargadi  Tinubu Kan Shirin Yakar Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da wa’adin da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta bai wa gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar, ya cika, fitaccen malamin Addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi kira ga shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya shiga yaki da kasar da ke makwabtaka da Nijeriya.

Shahararren malamin, wanda shi ne shugaban darikar Tijjaniya a Nijeriya, ya kuma bukaci majalisar dokokin kasar nan da kada ta amince da bukatar da shugaban kasar ya gabatar mata kan yakar Nijar.

  • AU, UN Da ECOWAS Sun Garzaya Nijar Don Tattaunawa Da Sojin Juyin Mulki
  • Kwatsam Ta Zayyana Ƙa’idoji Kafin Fara Shigo Da Kayayyaki Daga Iyakoki

A cewar dattijon malamin, maimakon su shiga yaki da kasar, kamata ya yi shugaba Tinubu da sauran shugabannin ECOWAS su tattauna da gwamnatin mulkin sojan Nijar da ta hambarar da shugaba Mohammed Bazoum.

Sheikh Bauchi ya bayyana haka ne a Bauchi a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida, inda ya kara da cewa Nijeriya da Jamhuriyar Nijar na da dadaddiyar alakar da ke bukatar kara karfafa ta.

“’Yan Nijeriya da Nijar sun dade a tare. Don haka akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tsunduma cikin harkokin diflomasiyya da nufin karfafa kyakkyawar alakar bunkasar tattalin arziki da ci gaban kasashen Afirka ta Yamma,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

A cewar Shehin malamin, ya yi gargadin cewa, “yana da kyau a samar da wani kuduri na aminci don kaucewa zubar da jinin wadanda ba su ji ba ba su gani ba. ”

Daga nan sai ya bukaci sauran shugabannin Afirka ta Yamma da sauran masu ruwa da tsaki da su rungumi tattaunawa ta diflomasiya.

“Muna kira ga Shugaba Tinubu; Muna kuma kira ga Majalisar Dokoki ta kasa da dukkan shugabannin ECOWAS da masu ruwa da tsaki da kada su shiga da Nijar.

“Wannan kudirin ne na ceto rayukan wadanda ba su ji ba ba su gani ba, da kuma ceto mutane daga shiga cikin kuncin rayuwa,” in ji Sheikh Dahiru Bauchi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASJuyin MulkiNijarSheikh Dahiru BauchiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

AU, UN Da ECOWAS Sun Garzaya Nijar Don Tattaunawa Da Sojin Juyin Mulki

Next Post

Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

Related

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
Labarai

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

2 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

3 hours ago
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
Labarai

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

5 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

6 hours ago
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

14 hours ago
Tinubu
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

15 hours ago
Next Post
Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

LABARAI MASU NASABA

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana

September 16, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa

September 16, 2025
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

September 15, 2025
Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 

September 15, 2025
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

September 15, 2025
Tinubu

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Yanke Hutu, Zai Dawo Abuja Gobe Talata

September 15, 2025
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.