• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin jiya Talata ne aka rufe gasar daliban jami’o’in kasa da kasa ko FISU kaso na 31, a filin taro na kade-kade dake birnin Chengdu, fadar mulkin lardin Sichuan dake kudu maso yammacin kasar Sin.

Gasar wadda ta gudana tsakanin ranaikun 28 ga watan Yuli zuwa 8 ga watan Agustan nan. Gasar ta hallara jimillar ’yan wasa 6,500 daga kasashe da yankuna 113, wadanda suka fafata a fannoni 269 na wasanni 18, tare da karya matsayin bajimta sau 22, cikin kwanaki 12 na gudanarta.

  • Jami’ar FISU: Tawagogin Dake Halartar Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa Ta Chengdu Sun Yaba Da Yadda Wasannin Ke Gudana

’Yar wasan ninkaya ta kasar Sin ajin mata Zhang Yufei, ta kafa tarihin zama mafi samun lambobin yabo a gasar, inda ta kammala da lambobin zinari 9 a dukkanin gasannin da ta fafata.

A bangaren tawagar kasar Sin mai mutane 411, an zabo sama da rabin daliban dake cikinta ne ta hanyar gwajin kwazonsu a mataki na kasa, sun kuma lashe lambobin yabo 178, ciki har da lambobin zinari 103, matakin da ya sanya su kasancewa kan gaba, a fannin lashe lambobin yabo a gasar, baya ga sauran ’yan wasa daga kasashe da yankuna 53, wadanda su ma suka lashe lambobin yabo daban daban, ciki har da 35, wadanda ’yan wasansu suka lashe a kalla lambar zinari daya.

Dan majalissar gudanarwar kasar Sin Shen Yiqin, da mukaddashin shugaban gasar ta FISU Leonz Eder, da babban shugaban kwamitin shirya gasar ta birnin Chengdu Huang Qiang, sun halarci bikin rufe gasar.

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

A jawabin da ya gabatar, mista Eder ya ayyana rufe gasar, tare da jinjinawa mashiryanta bisa kwazonsu na ganin gasar ta kammala cikin nasara.

Bayan gasar wadda birnin Beijing ya karbi bakunci a shekarar 2001, da wacce birnin Shenzhen ya karbi a bukunci a shekarar 2011, a wannan karo birnin Chengdu, mai tarihin shekaru 2,300 da kafuwa, wanda kuma ke kudu maso yammacin kasar Sin, ya zamo birni na 3 da ya karbi bakuncin gasar ta lokacin zafi, mai gudana duk bayan shekaru biyu-biyu. Kaza lika, wannan ne karon farko da wani birni dake yammacin kasar Sin ya karbi bakuncin babbar gasar wasannin motsa jiki ta kasa da kasa a kasar ta Sin.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 

Next Post

Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

Related

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

15 hours ago
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

16 hours ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

17 hours ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

18 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

19 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

21 hours ago
Next Post
Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

LABARAI MASU NASABA

FISU

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
FISU

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.