• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da yammacin jiya Talata ne aka rufe gasar daliban jami’o’in kasa da kasa ko FISU kaso na 31, a filin taro na kade-kade dake birnin Chengdu, fadar mulkin lardin Sichuan dake kudu maso yammacin kasar Sin.

Gasar wadda ta gudana tsakanin ranaikun 28 ga watan Yuli zuwa 8 ga watan Agustan nan. Gasar ta hallara jimillar ’yan wasa 6,500 daga kasashe da yankuna 113, wadanda suka fafata a fannoni 269 na wasanni 18, tare da karya matsayin bajimta sau 22, cikin kwanaki 12 na gudanarta.

  • Jami’ar FISU: Tawagogin Dake Halartar Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa Ta Chengdu Sun Yaba Da Yadda Wasannin Ke Gudana

’Yar wasan ninkaya ta kasar Sin ajin mata Zhang Yufei, ta kafa tarihin zama mafi samun lambobin yabo a gasar, inda ta kammala da lambobin zinari 9 a dukkanin gasannin da ta fafata.

A bangaren tawagar kasar Sin mai mutane 411, an zabo sama da rabin daliban dake cikinta ne ta hanyar gwajin kwazonsu a mataki na kasa, sun kuma lashe lambobin yabo 178, ciki har da lambobin zinari 103, matakin da ya sanya su kasancewa kan gaba, a fannin lashe lambobin yabo a gasar, baya ga sauran ’yan wasa daga kasashe da yankuna 53, wadanda su ma suka lashe lambobin yabo daban daban, ciki har da 35, wadanda ’yan wasansu suka lashe a kalla lambar zinari daya.

Dan majalissar gudanarwar kasar Sin Shen Yiqin, da mukaddashin shugaban gasar ta FISU Leonz Eder, da babban shugaban kwamitin shirya gasar ta birnin Chengdu Huang Qiang, sun halarci bikin rufe gasar.

Labarai Masu Nasaba

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

A jawabin da ya gabatar, mista Eder ya ayyana rufe gasar, tare da jinjinawa mashiryanta bisa kwazonsu na ganin gasar ta kammala cikin nasara.

Bayan gasar wadda birnin Beijing ya karbi bakunci a shekarar 2001, da wacce birnin Shenzhen ya karbi a bukunci a shekarar 2011, a wannan karo birnin Chengdu, mai tarihin shekaru 2,300 da kafuwa, wanda kuma ke kudu maso yammacin kasar Sin, ya zamo birni na 3 da ya karbi bakuncin gasar ta lokacin zafi, mai gudana duk bayan shekaru biyu-biyu. Kaza lika, wannan ne karon farko da wani birni dake yammacin kasar Sin ya karbi bakuncin babbar gasar wasannin motsa jiki ta kasa da kasa a kasar ta Sin.(Saminu Alhassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Za Mu Tabbatar An Zakulo Makasan Sheikh Albani Kuri – Gwamnan Gombe 

Next Post

Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

Related

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

2 hours ago
Kayan Aro Baya Rufe Katara
Daga Birnin Sin

Kayan Aro Baya Rufe Katara

3 hours ago
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

4 hours ago
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 
Daga Birnin Sin

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

5 hours ago
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

6 hours ago
Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gabatar Da Shagulgulan Al’adu Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Samun Nasarar Yaki Da Zaluncin Japanawa

7 hours ago
Next Post
Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.