ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Kammala Gasar Fisu Karo Na 31 a Birnin Chengdu 

by CMG Hausa
3 years ago
FISU

Da yammacin jiya Talata ne aka rufe gasar daliban jami’o’in kasa da kasa ko FISU kaso na 31, a filin taro na kade-kade dake birnin Chengdu, fadar mulkin lardin Sichuan dake kudu maso yammacin kasar Sin.

Gasar wadda ta gudana tsakanin ranaikun 28 ga watan Yuli zuwa 8 ga watan Agustan nan. Gasar ta hallara jimillar ’yan wasa 6,500 daga kasashe da yankuna 113, wadanda suka fafata a fannoni 269 na wasanni 18, tare da karya matsayin bajimta sau 22, cikin kwanaki 12 na gudanarta.

  • Jami’ar FISU: Tawagogin Dake Halartar Gasar Wasannin Daliban Jami’o’in Kasa Da Kasa Ta Chengdu Sun Yaba Da Yadda Wasannin Ke Gudana

’Yar wasan ninkaya ta kasar Sin ajin mata Zhang Yufei, ta kafa tarihin zama mafi samun lambobin yabo a gasar, inda ta kammala da lambobin zinari 9 a dukkanin gasannin da ta fafata.

ADVERTISEMENT

A bangaren tawagar kasar Sin mai mutane 411, an zabo sama da rabin daliban dake cikinta ne ta hanyar gwajin kwazonsu a mataki na kasa, sun kuma lashe lambobin yabo 178, ciki har da lambobin zinari 103, matakin da ya sanya su kasancewa kan gaba, a fannin lashe lambobin yabo a gasar, baya ga sauran ’yan wasa daga kasashe da yankuna 53, wadanda su ma suka lashe lambobin yabo daban daban, ciki har da 35, wadanda ’yan wasansu suka lashe a kalla lambar zinari daya.

Dan majalissar gudanarwar kasar Sin Shen Yiqin, da mukaddashin shugaban gasar ta FISU Leonz Eder, da babban shugaban kwamitin shirya gasar ta birnin Chengdu Huang Qiang, sun halarci bikin rufe gasar.

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

A jawabin da ya gabatar, mista Eder ya ayyana rufe gasar, tare da jinjinawa mashiryanta bisa kwazonsu na ganin gasar ta kammala cikin nasara.

Bayan gasar wadda birnin Beijing ya karbi bakunci a shekarar 2001, da wacce birnin Shenzhen ya karbi a bukunci a shekarar 2011, a wannan karo birnin Chengdu, mai tarihin shekaru 2,300 da kafuwa, wanda kuma ke kudu maso yammacin kasar Sin, ya zamo birni na 3 da ya karbi bakuncin gasar ta lokacin zafi, mai gudana duk bayan shekaru biyu-biyu. Kaza lika, wannan ne karon farko da wani birni dake yammacin kasar Sin ya karbi bakuncin babbar gasar wasannin motsa jiki ta kasa da kasa a kasar ta Sin.(Saminu Alhassan)

FISU
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
Daga Birnin Sin

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
Daga Birnin Sin

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci
Daga Birnin Sin

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Next Post
Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

Masu Bincike Na Sin Sun Gano Kwayar Halitta Mai Kara Yawan Shinkafa

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.