• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Malamai Suka Dirar Wa Batun Yaki Da Nijar

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Yadda Malamai Suka Dirar Wa Batun Yaki Da Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Manyan malaman musulunci a Nijeriya sun yi kashedin afka wa Nijar da yaki sakamakon kin mayar da Shugaba Bazoum a bisa karagar mulki da sojojin juyin mulki suka yi. 

Idan dai za a iya tunawa dai, kungiyar ECOWAS ta yi ganawar gaggawa a cikin watan Agusta, inda ta bai wa sojojin juyin mulki da ke kasar Nijar kwanaki bakwai na su mika mulki ko su fuskanci takunkumai ciki har da barazanar daukar matakin karfin soja.

  • NSCDC Ta Lalata Haramtattun Matatun Mai 10, Ta Kafa ‘Yan Sintiri
  • Fasahar Aikin Gona Da Ire-Iren Hatsi Masu Inganci Na Sin A Bikin Baje Kolin Uganda

Da yake nashi gargadin, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi kira ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu da ka da ya shiga yaki da kasar da ke makwabtaka da Nijeriya.

Shahararren malamin, ya kuma bukaci majalisar dokokin kasar nan da ka da ta amince da bukatar da shugaban kasar ya gabatar mata kan yakar Nijar.

A cewar dattijon malamin, maimakon su shiga yaki da kasar, kamata ya yi Shugaba Tinubu da sauran shugabannin ECOWAS su tattauna da gwamnatin mulkin sojan Nijar da ta hambarar da shugaba Bazoum.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

“’Yan Nijeriya da Nijar sun dade a tare. Don haka akwai bukatar gwamnatin tarayya ta bi hanyoyin diflomasiyya da nufin karfafa kyakkyawar alaka da bunkasa tattalin arziki da ci gaban kasashen yammacin Afirka,” in ji shi.

A nasa bargaren, Dakta Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya gargadin cewa, mutane a hankali da lallashi ake bin su wajen cimma wani lamari da kuma kula da lamarinsu, ba a son gaggawa da ganganci a cikin harkokin mulki.

Ya ce dokokin kungiyar ECOWAS sun tsara cewa duk abin da ya faru a cikin gidan wata kasa bai shafi wata kasa ba, saboda haka a bar mutane su zabi hanyar da suke so, don haka idan aka ce za a afka wa kasar Nijar da yaki domin wani abu da mutanen kasar suka yi, wannan babban kuskure ne.

Ya kara da cewa kar gwamnati ta sake da dauki wannan mummunan hanyar, sai dai a ja kunnansu kan wannan juyin mulki. Ya ce ‘yan siyasan afirka har yau ba su balaga ba, suna nan a matsayin kananan yara wanda suke kuntata wa mutanensu ta hanyar rashin kula da jin dadin al’umma.

Dakta Gumi ya ce idan da ‘yan siyasan suka balaga za su iya gudanar da harkokin mulki ta yadda babu wanda zai yi musu juyin mulki.

Har ila yau, jagoran Harkar Musulunci a Nijeriya, Sheikh Ibraheem Zakzaky, ya yi gargadin cewa Faransa da Amurka ne suke son amfani da Nijeriya wajen kai wa Nijar hari, yana mai bayyana yadda kasashen biyu suka zama danjuma da danjummai.

“Ko da ‘yan kudancin Nijeriya ba sa Kallon Nijar da Nijeriya a matsayin daya, su ‘yan arewa haka yake a wurinsu… Gazargamu ita ce shalkwatar Daular Kanem Borno har yanzu akwai ragowar gine-gine na tarihi, ko da aka kacancana mu ba a rushe mana tarihi ba, wasu yankuna suna Nijar wasu suna Nijeriya… Haka idan aka duba iyakokin Daular Shehu Usman daga Borno zuwa Sakkwato, kowane gari an dare shi gida biyu. Idan aka duba iyakokin Hadejia, wasu an raba an ba Nijar. Akwai wani yanki na Gumel da yake Nijar. Idan ka tsallaka iyakar kasa ta Maigatari har yanzu dai kana cikin yankin Gumel ne amma an bai wa Nijar. Haka nan Daular Gobir an kacancana ta ce a tsakanin Nijar da Nijeriya… Mahaifar Shehu Usman Danfodiyo, Marata a Nijar take. Dangantakar da ke tsakanin Nijar da Nijeriya ta fi karfin tunani,” in ji sanarwar da ya fitar.

Wakazalika, Majalisar Malaman Nijeriya ta nemi a dakatar da batun daukar matakin soja domin warware matsalar ta Nijar.

Malaman sun ce matakin ba zai haifar da sakamako mai kyau ga kasashen biyu ba. Sun nemi kowane bangare da ya dauki matakin salama cikin yanayin diflomasiyya domin tallafa wa Jamhuriyar Nijar da mutanenta.

Wannan na zuwa ne bayan wata ganawa da kungiyar ta yi, inda shugabanta Aminu Inuwa Muhammad da sakatarenta, Injiniya Basheer Adamu Aliyu suka fitar da wata sanarwa a kan matsayar da suka cimma.

“Yana da kyau gwamnatin Nijeriya ta sake yin duba kan kokarin da ta ke yi, sannan kuma ga barazanar tsaro ta ko ina, wadanda su ke ta tatse ‘yar lalitar kasar, kada a afka mu cikin wani rikici da za mu iya kaucewa, kawai don mu farantawa wasu kasashen duniya a siyasance.”

Malaman da suka sanya hannu kan takardar a yayin zaman sun kai 25 daga sassa daban-daban na kasar nan, inda suka yi fatan cewa barazanar da ake gani a zahirance ba zai kai ga janyo barakar zaman lafiya a tsakanin Nijeriya da Nijar ba.

Majalisar ta jadadda goyon bayan matakan diflomasiyya da a ka fara dauka ta hanyar aikewa da wakilai domin zama da jagororin sojin juyin mulkin Nijar don tattaunawa cikin salama.

“Juyin mulkin da aka yi a Jamhuriyar Nijar da ma duk wadanda a ka yi a sauran kasashen yankin SAHEL abun takaici ne, kuma ya cancanci duk masu ra’ayin dimokuradiyya su yi tir da shi da ma duk masu neman zaman lafiya a duniya.

“Duk da cewa mutane da dama na fifita dimokradiyya da tsare-tsarenta, amma hanyar samar da shugabanci na gari, abu ne da ya kebanci mutanen kowace kasa su kadai. Don haka damar mutanen Jamhuriyyar Nijar ce su bi duk hanyoyin da su ka ga sun dace domin dawo da dimokradiyya a kasarsu, idan sun ga hakan ya dace; kuma duk wani kokarin da wani zai yi, a ko ina yake, matukar ba mutanen Nijar ba, abu ne da zai yi karan tsaye ga dimokradiyya da sunan samar da dimokradiyya.” In ji majalisar.

 A ranar Juma’ar makon da ya gabata, manyan hafsoshin sojin wasu kasashen yammacin Afirka sun amince da daukar matakin soja idan har aka kasa shawo kan lamarin ta hanyar diflomasiyya.

Hafsoshin sojojin sun hada da na kasashen Togo, Sierra Leone, Senegal, Nijeriya, Ghana, Liberiya, Guinea Bissau, Gambia, Cote D’iboire, Cabo Berde da kuma Jamhuriyar Benin, wanda suka bayyana haka jim kadan bayan ganawar da suka yi a Abuja.

Domin mayar da martani, gwamnatin mulkin sojar a Jamhuriyar Nijar ta rufe sararin samaniyar kasar sakamakon barazanar daukar matakin soji da kungiyar ECOWAS ta yi.

Wannan lamari na juyin mulki ya kara dawo da hannun agogo baya, a daidai lokacin da kasashen waje ke ci gaba da kwashe ‘yan kasarsu daga Nijar tare da yi musu gargadin kar su kuskura su ziyarci kasashen Burkina Faso da Mali, wanda kasashe ne da sojoji suka yi juyin mulki a yankin Afirka cikin ‘yan shekarun nan.

Jamus da Italiya dai sun yi kira ga ECOWAS ta kara tsawaita wa’adin da ta bai wa sojojin juyin mulkin na dawo da mulkin dimokuradiyya.

Tuni dai kasashen Mali da Burkina Faso suka ayyana goyon bayansu ga sojojin juyin mulkin na Nijeriya yayin da suka bayyana cewa afka wa Nijar da yaki tamkar afka musu ne kuma ba za su rungume hannu suna kallo ba, za su taya Nijar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Kallon-Kallo: Kungiyar Kwadago Da ‘Yan Nijeriya (2)

Related

Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

9 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

12 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

14 hours ago
Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano
Manyan Labarai

Ƙungiyoyin Farar Hula Sun Nemi A Dakatar Da Jami’an Gwamnatin Kano

20 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Kama Wani Gawutaccen Ɗan Fashi Da Garkuwa Da Mutane A Nasarawa

1 day ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

2 days ago
Next Post
Kallon-kallon: Kungiyar ‘Yan Kwadago Da ‘Yan Nijeriya

Kallon-Kallo: Kungiyar Kwadago Da ‘Yan Nijeriya (2)

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.