• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kamfanin Gine-gine Na CITIC Ya Mika Sashen Karshe Na Aikin Ginin Babbar Hanyar Mota A Aljeriya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kamfanin Gine-gine Na CITIC Ya Mika Sashen Karshe Na Aikin Ginin Babbar Hanyar Mota A Aljeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A jiya Asabar ne kamfanin gine gine na kasar Sin CITIC, ya mika sashen karshe na aikin ginin babbar hanyar mota da ta hade sassan larduna 17 dake kasar Aljeriya. Karkashin babban aikin ginin hanyar, CITIC ya kammala ginin kilomita 84 na hanyar.

Hanyar wadda ta hade sassan gabashi da yammacin kasar, ta dangana daga birnin Drean na lardin El Tarf a gabas mai nisa, zuwa birnin Raml Souk mai iyaka da kasar Tunisiya.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Gaggauta Gyara Kura-Kurai Da Bin Ka’idojin WTO

Yayin bikin kaddamar da sashen karshe na wannan katafaren aiki a birnin El Tarf, firaministan Aljeriya Aymen Benabderrahmane, ya jinjinawa muhimmin matsayin wannan aiki, wanda ya ce zai saukaka zirga zirgar matafiya, ta bunkasa hada hadar tattalin arziki tsakanin al’ummun Aljeriya da na Tunisiya.

Benabderrahmane, ya kuma yabi ingancin aikin hanyar, yana mai cewa, injiniyoyin kasar Aljeriya, da ‘yan kwadago da suka shiga aka dama da su a aikin, sun samu karin kwarewa da sanin makamar aiki.

Yayin bikin kaddamarwar, mataimakin babban manajan kamfanin CITIC a kasar Aljeriya Qi Shujie, ya ce injiniyoyin kasar Sin sun fuskanci manyan kalubale yayin da suke gudanar da aikin, ciki har da bukatar gudanar da ciko mai tarin yawa, da matsalar zaftarewar kasa, tun fara aikin ginin kilomita 84n a shekar 2017, amma duk da haka, sun kai ga kammala aikin a kan lokaci.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Kaza lika, wata sanarwa da kamfanin na CITIC ya fitar, ta ce kamfanin ya sauke nauyin dake wuyan sa, yayin da yake gudanar da ginin hanyar, wanda ya kunshi kafa cibiyar jagoranci, da ta lura da nagartar aiki, kana ya horas da dubban ma’aikatan hanya na kasar ta Aljeriya.

Har ila yau, kamfanin ya gudanar da ayyukan tallafawa al’ummun dake makwaftaka da aikin, ciki har da shiga ayyukan bunkasa jin dadin jama’a, kamar bayar da tallafi ga iyalai mabukata yayin azumin watan Ramadan, da gina filayen dakile yaduwar gobar daji, da samar da daukin ambaliyar ruwa. (Saminu Alhassan)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Bindiga Sun Banka Wa Fadar Basarake Wuta A Jihar Imo

Next Post

‘Yansanda Sun Cafke Wani Dan Tsibbu Da Kan Mutum A Jihar Ondo 

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

8 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

9 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

10 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

11 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

12 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Wani Dan Tsibbu Da Kan Mutum A Jihar Ondo 

'Yansanda Sun Cafke Wani Dan Tsibbu Da Kan Mutum A Jihar Ondo 

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.