ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

by Abba Ibrahim Wada
9 months ago
Ballon D'Or

Kyautar lashe gasar Ballon d’Or yanzu ta zama kyautar da take auna kokarin dan wasa ko kuma wadda take fayyace dan wasan da ya fi nuna bajinta a duniyar kwallon kafa musamman a tsakanin matasa.

A karshen watan da ya gabata ne aka yi bikin karrama gwarzon ‘yankwallon kafa na duniya na shekarar 2025, inda aka karrama fitattun ‘yanwasa da suka nuna bajinta da kwarewa a kungiyoyi da kasashensu a kakar da ta wuce. Kyautar Ballon d’Or, karramawa ce da take da matukar tasiri a kwallon kafa, inda duk da cewa hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA tana karrama gwarazan da take gani su ne kan gaba a duniya, an fi kallo tare da amfani da karramawar ta Ballon d’Or a matsayin wadda ta fi daraja.

  • Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
  • Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

A taron na, fitaccen danwasan kasar Faransa da kungiyar PSG, Ousmane Dembele ya lashe kyautar ta bana a bikin wanda aka yi a dakin taro na Theatre du Chatelet da ke birnin Paris a kasar Faransa.

ADVERTISEMENT

Aitana Bonmati ce ta lashe Ballon d’Or ta bangaren mata, wanda shi ne karo na uku da ta lashe kyautar a jere. Wani abu da ya ja hankalin masu bibiyar karramawar daga Nijeriya shi ne yadda mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta mata wato Super Falcons, Chiamaka Ndanozie ta zo ta hudu a cikin masu tsaron raga mata a duniya.

Wadanne fitattun ‘yan kwallon kafan Nijeriya ne suka kusa lashe kambun a tarihin karramawar?

LABARAI MASU NASABA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

BICTOR IKPEBA – 1997

Dan wasan Nijeriya Bictor Ikpeba, ne da ake yi wa lakabi da suna “Prince of Monaco,” Ikpeba ya samu shiga ne bayan ya taimaka wa kungiyar Monaco ta samu nasarar lashe kofin Ligue 1 ta Faransa. Danwasan ya samu kuri’a 2, inda ya kare a mataki na 32 a cikin jerin wadanda suka samu karramawa a shekarar ta 1997.

ADEMOLA LOOKMAN – 2024

A kakar bara, wanda ya lashe gwarzon dan kwallon kafa na Afirka, Ademola Lukman, wanda a lokacin yake buga wasa a kungiyar Atalanta ne ya zo na 14 a bikin karramawar. Lookman ya lashe gasar Europa da Atalanta, inda ya zura kwallo uku rigis a raga, sannan ya taka rawar gani sosai a gasar cin kofin Afirka.

FINIDI GEORGE – 1995

Finidi George danwasan Nijeriya ne da ya yi tashe sosai a shekarun baya a Nijeriya da kungiyoyin Turai. Ya samu shiga cikin zaratan ‘yankwallo na duniya ne a shekarar 1995 bayan nasarar da ya samu a kungiyar Ajad ta Holland, inda ya samu shiga cikin jerin bayan an fadada karramawar zuwa kasahen da ba na turai ba.

A gasar Champions League ta shekarar 1995, Finidi ya zura kwallo tara, sannan ya bayar aka zura kwallo 11 kuma a shekarar ne Ajad ta lashe gasar Champions League da gasar Eredibisie ta kasar Holland da wasu kofuna uku. Amma a shekarar dan wasa Finidi ya kare a mataki na 21 a shekarar 1995.

BICTOR OSIMHEN – 2023

Danwasan kwallon gaba na Nijeriya wanda a yanzu haka yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Galatassary ya samu shiga ne bayan ya taimaka wa kungiyar Napoli wajen lashe gasar Serie A karon farko a shekara 33, sannan ya lashe wanda ya fi zura kwallo a shekarar ta 2023.

A shekarar ce Osimhen ya zo na takwas a duniya sannan kuma duka a shekarar dan wasa Bictor Osimhen shi ne ya lashe gwarzon dankwallon Afirka mafi kwarewa a shekarar 2023.

NWANKWO KANU – 1996 DA 1999

Shahararren dan wasa Nwankwo Kanu na cikin zaratan ‘yankwallo kafa ‘yan Nijeriya suka dade suna jan zarensu a harkar tamaula. A shekarar 1996, Kanu ya samu kuri’a 14, inda ya zo na 11 bayan ya lashe kofin Olympic da aka buga a Atlanta, da kuma rawar da ya taka a kungiyar Inter Milan ta Italiya.

Haka kuma a lokacin da ya koma Arsenal, tsohon kyaftin din na Nijeriya ya sake samun shiga, inda a shekarar 1999 ya zo na 23 a duniya. Sanan tsohon danwasan na Arsenal ya lashe karramawar gwarzon dankwallon Afirka sau biyu a shekarun 1996 da 1999.

ASISAT OSHOALA – 2022 DA 2023

Mace mai kamar maza, Asisat Oshoala ita ce ‘yarkwallon Nijeriya mace da ta fi lashe kambun gwarzuwar kwallon kafa ta Afirka. Sannan ita ce mace ta farko daga Nijeriya da ta fara shiga jerin wadanda aka karrama a Ballon d’Or ta mata. Bayan lashe gasar Champions League ne ta zama gwarzuwa ta 16 a duniya a shekarar 2022, sannan ta sake zuwa ta 20 a shekarar 2023.

CHIAMAKA NNADOZIE – 2025

A bikin karramawar ta bana kuma, mai tsaron ragar kungiyar Brighton & Hobe Albion ta Ingila, Chiamaka Nnadozie ce ta samu tagomashi, inda ta zo ta hudu a cikin masu tsaron raga mata a duniya, wanda shi ne matsayi mafi girma da Nijeriya ta taba samu a karramawar. Chiamaka Nnadozie ta lashe kofin gasar cin kofin Afirka na mata sau biyu a 2018 da 2024.

A Afirka dai an samu dan wasa George Weah, dan kasar Liberiya wanda ya taba lashe kyautar Ballon d’Or a duniya, kuma tun daga wancan lokacin har yanzu ba a sake samun wani dan wasa daga nahiyar Afirka ba da ya sake lashe kyautar.

Ballon D'Or
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
  • Abba Ibrahim Wada
    FIFA Za Ta Biya Omar Artan Alawus Ɗin Da Za A Bai Wa Kowanne Alƙalin Wasa
  • Abba Ibrahim Wada
    Duk Da Rashin Halartar ‘Super Eagles’ Gasar Kofin Duniya, Nijeriya Ba Ta Rasa Wakilai Ba
  • Abba Ibrahim Wada
    Su Waye Wakilan Afirka A Kofin Duniya?

MASU ALAKA

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino
Wasanni

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya
Wasanni

Lionel Messi Ya Kafa Tarihin Wanda Yafi Kowa Zura Kwallaye A Tarihin Gasar Cin Kofin Duniya

June 22, 2026
Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada
Wasanni

Ɗanwasa Thomas Partey Ya Yi Rashin Nasara A Kotun Canada

June 21, 2026
Next Post
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.