ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

by Abba Ibrahim Wada
8 months ago
Ballon D'Or

Kyautar lashe gasar Ballon d’Or yanzu ta zama kyautar da take auna kokarin dan wasa ko kuma wadda take fayyace dan wasan da ya fi nuna bajinta a duniyar kwallon kafa musamman a tsakanin matasa.

A karshen watan da ya gabata ne aka yi bikin karrama gwarzon ‘yankwallon kafa na duniya na shekarar 2025, inda aka karrama fitattun ‘yanwasa da suka nuna bajinta da kwarewa a kungiyoyi da kasashensu a kakar da ta wuce. Kyautar Ballon d’Or, karramawa ce da take da matukar tasiri a kwallon kafa, inda duk da cewa hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA tana karrama gwarazan da take gani su ne kan gaba a duniya, an fi kallo tare da amfani da karramawar ta Ballon d’Or a matsayin wadda ta fi daraja.

  • Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
  • Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

A taron na, fitaccen danwasan kasar Faransa da kungiyar PSG, Ousmane Dembele ya lashe kyautar ta bana a bikin wanda aka yi a dakin taro na Theatre du Chatelet da ke birnin Paris a kasar Faransa.

ADVERTISEMENT

Aitana Bonmati ce ta lashe Ballon d’Or ta bangaren mata, wanda shi ne karo na uku da ta lashe kyautar a jere. Wani abu da ya ja hankalin masu bibiyar karramawar daga Nijeriya shi ne yadda mai tsaron ragar kungiyar kwallon kafa ta mata wato Super Falcons, Chiamaka Ndanozie ta zo ta hudu a cikin masu tsaron raga mata a duniya.

Wadanne fitattun ‘yan kwallon kafan Nijeriya ne suka kusa lashe kambun a tarihin karramawar?

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

BICTOR IKPEBA – 1997

Dan wasan Nijeriya Bictor Ikpeba, ne da ake yi wa lakabi da suna “Prince of Monaco,” Ikpeba ya samu shiga ne bayan ya taimaka wa kungiyar Monaco ta samu nasarar lashe kofin Ligue 1 ta Faransa. Danwasan ya samu kuri’a 2, inda ya kare a mataki na 32 a cikin jerin wadanda suka samu karramawa a shekarar ta 1997.

ADEMOLA LOOKMAN – 2024

A kakar bara, wanda ya lashe gwarzon dan kwallon kafa na Afirka, Ademola Lukman, wanda a lokacin yake buga wasa a kungiyar Atalanta ne ya zo na 14 a bikin karramawar. Lookman ya lashe gasar Europa da Atalanta, inda ya zura kwallo uku rigis a raga, sannan ya taka rawar gani sosai a gasar cin kofin Afirka.

FINIDI GEORGE – 1995

Finidi George danwasan Nijeriya ne da ya yi tashe sosai a shekarun baya a Nijeriya da kungiyoyin Turai. Ya samu shiga cikin zaratan ‘yankwallo na duniya ne a shekarar 1995 bayan nasarar da ya samu a kungiyar Ajad ta Holland, inda ya samu shiga cikin jerin bayan an fadada karramawar zuwa kasahen da ba na turai ba.

A gasar Champions League ta shekarar 1995, Finidi ya zura kwallo tara, sannan ya bayar aka zura kwallo 11 kuma a shekarar ne Ajad ta lashe gasar Champions League da gasar Eredibisie ta kasar Holland da wasu kofuna uku. Amma a shekarar dan wasa Finidi ya kare a mataki na 21 a shekarar 1995.

BICTOR OSIMHEN – 2023

Danwasan kwallon gaba na Nijeriya wanda a yanzu haka yake buga wasa a kungiyar kwallon kafa ta Galatassary ya samu shiga ne bayan ya taimaka wa kungiyar Napoli wajen lashe gasar Serie A karon farko a shekara 33, sannan ya lashe wanda ya fi zura kwallo a shekarar ta 2023.

A shekarar ce Osimhen ya zo na takwas a duniya sannan kuma duka a shekarar dan wasa Bictor Osimhen shi ne ya lashe gwarzon dankwallon Afirka mafi kwarewa a shekarar 2023.

NWANKWO KANU – 1996 DA 1999

Shahararren dan wasa Nwankwo Kanu na cikin zaratan ‘yankwallo kafa ‘yan Nijeriya suka dade suna jan zarensu a harkar tamaula. A shekarar 1996, Kanu ya samu kuri’a 14, inda ya zo na 11 bayan ya lashe kofin Olympic da aka buga a Atlanta, da kuma rawar da ya taka a kungiyar Inter Milan ta Italiya.

Haka kuma a lokacin da ya koma Arsenal, tsohon kyaftin din na Nijeriya ya sake samun shiga, inda a shekarar 1999 ya zo na 23 a duniya. Sanan tsohon danwasan na Arsenal ya lashe karramawar gwarzon dankwallon Afirka sau biyu a shekarun 1996 da 1999.

ASISAT OSHOALA – 2022 DA 2023

Mace mai kamar maza, Asisat Oshoala ita ce ‘yarkwallon Nijeriya mace da ta fi lashe kambun gwarzuwar kwallon kafa ta Afirka. Sannan ita ce mace ta farko daga Nijeriya da ta fara shiga jerin wadanda aka karrama a Ballon d’Or ta mata. Bayan lashe gasar Champions League ne ta zama gwarzuwa ta 16 a duniya a shekarar 2022, sannan ta sake zuwa ta 20 a shekarar 2023.

CHIAMAKA NNADOZIE – 2025

A bikin karramawar ta bana kuma, mai tsaron ragar kungiyar Brighton & Hobe Albion ta Ingila, Chiamaka Nnadozie ce ta samu tagomashi, inda ta zo ta hudu a cikin masu tsaron raga mata a duniya, wanda shi ne matsayi mafi girma da Nijeriya ta taba samu a karramawar. Chiamaka Nnadozie ta lashe kofin gasar cin kofin Afirka na mata sau biyu a 2018 da 2024.

A Afirka dai an samu dan wasa George Weah, dan kasar Liberiya wanda ya taba lashe kyautar Ballon d’Or a duniya, kuma tun daga wancan lokacin har yanzu ba a sake samun wani dan wasa daga nahiyar Afirka ba da ya sake lashe kyautar.

Ballon D'Or
Abba Ibrahim Wada
Website |  + postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    Ko Kasan ‘Yanwasan Da Za Su Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe?
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Ta Samu Lambobin Yabo 16 A Wasannin Tseren Keke
  • Abba Ibrahim Wada
    Nijeriya Za Ta Karbi Bakuncin Babban Taron Hukumar CAF Na Bana
  • Abba Ibrahim Wada
    Shin Ko Arsenal Za Ta Mamaye Duniya?

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya
Wasanni

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa
Wasanni

Galatasaray Ta Sanya Farashin Yuro Miliyan 150 Kan Osimhen, Chelsea Ta Nuna Sha’awar Ɗaukarsa

June 2, 2026
Next Post
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.