• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Ya Dace Nijeriya Ta Bi Sawun Kasashe Masu Shirin Fita Daga Kangin Dalar Amurka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yi hasashen dalar Amurka na iya kaiwa Naira 1,000 a kasuwannin canjin kudin Nijeriya, lamarin dake kara jefa fargabar karuwar tsadar rayuwa a zukatan ’yan Nijeriya. Kwan-gaba-kwan-bayan farashin dalar Amurka a Nijeriya sama da shekara 20 da suka gabata ya dankwafar da darajar Naira.

Majiyoyi daban-daban daga Bankin Duniya sun tabbatar da cewa harkokin shigo da kaya daga waje sun dara na fitar da su yawa a kasar. Na fitarwa wanda da su ake samun dalar, ba su wuce kashi 8.83% ba, na shigarwa kuma kashi 16.57%, sun kusan ninkawa.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Soke “Doka Game Da Taiwan”

Kasashe da dama sun fara farkawa daga baccin rafkana domin yi wa kansu mafita a kan kangin dalar Amurka. Tuni Argentina, Brazil da Bolivia dake nahiyar kudancin Amurka suka fara amfani da kudin kasar Sin, Renminbi a kasuwancinsu da Sin. Abin yana kara samun tagomashi a yankin Latin da Caribbean.

Wajibi ne kasashe su samar wa kansu mafita don rage dogaro da dalar Amurka sakamakon karuwar kudaden ruwa a kan dalar da ramewar asusun ajiyarsu na waje. Masana tattalin arziki na nuna cewa za a samu kasashen duniya da dama da za su rungumi amfani da kudin Sin RMB wajen huldar kasuwanci saboda kasancewar Sin a matsayin kasa mafi girman hada-hadar kasuwanci a duniya. Ko a kwanan baya, an ruwaito shugaban Brazil, Luiz Inacio Lula da Silva yana kiran kasashen duniya su samar wa kansu mafita a kan amfani da dalar Amurka, domin a cewarsa me ya sa dukkan kasashen duniya ke amfani da dalar a kasuwancinsu.

Bugu da kari, gwamnatocin kasashen waje da ke bukatar adana kudaden ajiyarsu na waje da dalar Amurka za su kara kashe kudi wajen neman dalar, inda lamarin zai fi shafar tattalin arzikin kasashe masu tasowa saboda ribar da ake samu wajen fitar da kaya zuwa waje ta ragu.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Haka zalika, Rasha da Sin sun cimma yarjejeniya don fara biyan kudin iskar gas da take samarwa kasar Sin a kudin Yuan da Rubles maimakon Dalar Amurka. Har ila yau, masu sayen man Rasha a Indiya suna biyan galibin kudin mai ne da ko dai kudin Rashar ko kuma Dirham na Hadaddiyar Daular Larabawa.

Yayin da wannan yunkuri na fita daga kangin dalar Amurka ke samun tagomashi, Kasashe masu kawancen bunkasa ci gabansu na BRICS (Brazil, Rasha, Indiya, Sin, da Afirka ta Kudu) suna shirin kaddamar da sabon kudin da kasashe mambobin kungiyar za su rika amfani da su wajen cinikayya a tsakaninsu. Haka nan gabanin taron kolin kungiyar BRICS na watan Agusta da za a yi a Afirka ta Kudu, yanzu haka akwai kasashe 24 da ke neman kulla kawance domin fita daga tarnakin da dalar Amurka ta yi musu na tsawon shekaru. Kasashen sun hada da Najeriya, Saudi Arabiya, Iran, Argentina, Hadaddiyar Daular Larabawa, Aljeriya, Masar, Bahrain, Indonesia da wasu kasashe na Afirka.

Ko a ’yan watannin baya, Kenya ta sauwake wa kanta nemo Dala Miliyan 500 duk wata don biyan kudin fetur da take shigo da shi, sakamakon kulla yarjejeniya da Kamfanin Mai na Saudiyya (Aramco) da na Abu Dhabi (Adnoc) da za su rika shigo mata da fetur da gas, ita kuma tana biya da kudin kasarta na Shillings.

Ya kamata Nijeriya ta dauki darasi ta farfado da yarjejeniyar musanyar kudin nan a tsakaninta da Sin ta kimanin Naira Biliyan 720 kwatankwacin RMB Biliyan 15 da aka kulla a 2018, saboda kasuwancin dake tsakaninsu wanda ko a watanni ukun farko na shekarar nan ya kai kimanin Naira Tiriliyan Hudu da Biliyan Hamsin da Biyar da Miliyan Dari Biyu da Talatin da Takwas (4,055,238,000.00), kamar yadda aka ruwaito Jami’ar Ofishin Jakadancin Sin a Legas, Ms. Yan Yuqing tana fada a ’yan watannin baya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'Yan Majalisar Dokokin NijeriyaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Za A Bude Bikin Baje Kolin Cinikayyar Hidima Na 2023 A Satumba

Next Post

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

9 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

10 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

11 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

12 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

13 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

1 day ago
Next Post
Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.