ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
3 years ago
Abuja

Kwamitin Majalisar Wakilai na wucin- gadi kan binciken dalilin tsaikon da aka samu wajen kammala tagwayen hanyar mota kilomita 375 daga Abuja- Kaduna- Kano ya fara gudanar da aikinsa tare da alwashin ganin an kammala aikin cikin lokaci.

Shugaban kwamitin na wucin-gadi, Hon. Abdussamad Dasuki ya bayyana cewar ko kadan ba su da manufar bita- da- kulli ga kowa a binciken illa domin shawo kan kalubalen da ke akwai na tsaikon kammala hanyar wadda Gwamnatin Tarayya ta sake bayar da kwangilar shimfidawa a 2020.

  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Yi Bincike Kan Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau
  • Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince Da Kwamishinoni 13

Hon. Dasuki wanda ya jagoranci manbobin kwamitin a ziyarar gani da ido a babbar muhimmiyar hanyar, ya kuma bayyana cewar binciken na da manufar ganin an aiwatar da dukkanin sharuda da ka’idojin da aka shata a kwangilar.

ADVERTISEMENT

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewar a yayin rangadin, kwamitin karara ya nuna rashin gamsuwa kan yadda akin ke tafiya da nuna damuwa kan yiyuwar kammala aikin a sabon wa’adin 2025 da Ma’aikatar Ayyuka ta ayyana.

Tun da farko, kwamitin ya gayyaci kamfanin Julius Berger da ke aiwatar da kwangilar da jami’an Ma’aikatar Ayyuka domin jin ta bakin su kan dalilin da yasa duk da makuddan kudaden da aka fitar kan aikin, amma aikin yana nesa ga wa’adin kammalawa. Jami’in kamfanin ya bayyana cewar aikin ya samu tsaiko ne a dalilin rashin tsaro da ke akwai a hanyar.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

A zaman tattaunawa da jami’an Ma’aikatar Ayyuka da kwamitin ya gudanar a karkashin jagorancin Hon. Dasuki, Babbar Sakataren Ma’aikatar, Mamuda Mamman ya bayyanawa kwamitin cewar an kusa kammala aikin sashe na 2 da na 3 na hanyar.

Ya bayyana cewar aikin hanyar a sashen Abuja- Kaduna ya fuskanci matsalar aiwatarwa ta kudi da matsalolin tsaro. Ya ce kusan kashi 20% ne a ka kammala a sashe na 1 daga Abuja zuwa Kaduna, amma ya baiwa kwamitin tabbacin kammala aikin a Mayu 2025.

A yanzu haka dai Kwamitin dai na wucin-gadi yana ci-gaba da aiwatar da aikinsa tare da tsammanin kai rahoto ga Majalisar Wakilai a cikin wa’adin makwanni hudu da majalisa ta baiwa kwamitin.

Abuja
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    2027:Cece-kuce Ta Barke Tsakanin Tinubu Da Atiku
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Yadda Rikici Ya Tsananta Tsakanin Dan Daba Da Malaman Addini A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dalilin Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Yankin Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Atiku Ya Koka Kan Ƙaruwar Ta’addanci A Sakkwato

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.