• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ganduje Ya Bukaci ‘Yan Majalisar Dokokin APC Su Goya Wa Abba Baya

by Abubakar Abba
2 years ago
in Siyasa
0
Abba Na Kokarin Fara Mulkin Kano Da Kuskure —Ganduje
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban jami’yyar APC na kasa, Abdullahi Ganduje, ya bukaci ‘yan majalisar dokokin APC 14 na jihar Kano da su mara wa gwamnatin Abba Kabir Yusuf domin ci gaban jihar. 

Yusuf dai, ya kasance dan jami’yyar adawa ta NNPP wanda kuma akwai zazzafar adawar siyasar a tsakaninsa da Ganduje tsohon gwamnan jihar Kano.

  • Cinikin Maguire daga Manchester United Zuwa West Ham Ya Lalace
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Ango Da Amarya A Filato

Ganduje ya bayyana hakan ne a ranar Litinin lokacin da ‘yan majalisar dokokin jihar suka je sakatariyar APC ta kasa da ke Abuja domin ta ya shi murnar zama shugaban APC na kasa.

Ya yi nuni da cewa, mara wa gwamnan jami’yyar adawa, ba wai hakan na nuna cewa sun bar dangantakarsu a matsayin ya’yan APC ba ne.

Ya kara cewa, gwamnan jihar mai ci daga wata jami’yyar ya fito, amma ina son ku sani cewa, ribar siyasa, shi ne bunkasa rayuwar al’umma saboda haka, ina ba ku shawara cewa, duk da banbancin siyasa, ku mara wa gwamnatin jihar mai ci baya don a ciyar da jihar gaba.

Labarai Masu Nasaba

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

Kazalika Ganduje ya ce, mara wa gwamnatin ta Yusuf baya, ba wai hakan zai dakatar da ku daga ci gaba da rike matsayinku na ‘yan majalisar dokokin jihar Kano ba ne har ila yau, yin hakan ba zai dakatar da mu daga yin aiki a tare domin mu sake kafa gwamnatin APC a jihar ba ne.

A cewarsa, abin da ke da muhimmanci ga al’ummar jihar, shi ne a samar musu da romon dimokuradiyya.

Bugu da kari, ya ce ina baku tabbacin cewa, za mu ba ku dukkan goyon bayan domin mu kara samun karin wasu ‘yan majalisar dokoki a jihar da kuma sake samun kafa wata sabuwar gwamnatin APC a Kano.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AbbaAPCGandujekanoNNPPSiyasa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Cinikin Maguire daga Manchester United Zuwa West Ham Ya Lalace

Next Post

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Kai Kashi 24.08

Related

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

14 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

17 hours ago
INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
Siyasa

INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027

2 days ago
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
Siyasa

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

3 days ago
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
Siyasa

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

3 days ago
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
Siyasa

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

4 days ago
Next Post
Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Kai Kashi 21.82 – NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Kai Kashi 24.08

LABARAI MASU NASABA

Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

Sin Na Goyon Bayan Duk Wani Mataki Na Warware Batun Ukraine Ta Hanyar Lumana

August 12, 2025
EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

EFCC Ta Bayar Da Belin Tambuwal, Ta Yi Allah-wadai Da Zargin Da Jam’iyar ADC Ta Yi

August 12, 2025
Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

Babu Neman Afuwa Kan Nuna Goyan Bayan Tinubu Da Na Yi – Soludo

August 12, 2025
Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

Ilimin Fasahar Zamani Dama Ce Ta Samun Kyakkyawar Makoma A Afrika

August 12, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.