ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, July 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi

by Abubakar Sulaiman
10 months ago
PDP

Shugaban Gwamnonin Jam’iyyar PDP (PDP Governors Forum) kuma Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya bayyana cewa barin jam’iyya saboda wasu mutane alamar rashin jarumta ce. Ya ce duk wanda ya bar PDP saboda matsalar cikin gida hakan na nuni da gaza jurewa gwagwarmaya ta siyasa.

Gwamna Mohammed ya kuma tabbatar da cewa babban taron gangamin jam’iyyar na ƙasa (National Convention) da za a gudanar a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 ga Nuwamba, zai gudana kamar yadda aka tsara duk da ƙalubalen da ake fuskanta. Ya bayyana haka ne yayin ƙaddamar da kwamiti na taron jam’iyyar.

  • Arewa Ta Daina Zama Ci-Ma Zaune A Tattalin Arziƙi – Gwamnan Bauchi
  • Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Rahotanni sun nuna cewa Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, zai sanar da barin PDP a ranar Talata mai zuwa, yayin da ake hasashen Gwamnan Bayelsa, Douye Diri, da Gwamnan Taraba, Agbu Kefas, ma na iya bin sahu. A baya, Gwamnonin Akwa Ibom da Delta, Umo Eno da Sheriff Oborevwori, sun bar jam’iyyar.7

ADVERTISEMENT

Gwamna Mohammed ya jaddada cewa mambobin PDP su kasance masu ƙwarin guiwa, su guji damuwa da ficewar wasu daga cikin jam’iyyar. “Abin da ke nuna jarumta shi ne kasancewa da jam’iyya don a fuskanci ƙalubale. Barin jam’iyya saboda mutum ɗaya ko mace ɗaya ba jarumta ba ce,” in ji shi

Ya kuma sha alwashin cewa babban taron jam’iyyar zai gudana kamar yadda aka tsara, yana mai cewa, “Mun sha wahala a jam’iyya amma muna daurewa. Ba wanda zai hana wannan taro gudana. Idan magauta suka ci nasara akan PDP, to Nijeriya gaba ɗaya ta shiga duhu.” Gwamnan ya kuma caccaki gwamnatin APC, yana cewa tun bayan da PDP ta bar mulki a 2015, Nijeriya ba ta sake samun nagartacciyar gwamnati ba.

LABARAI MASU NASABA

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

PDP
Abubakar Sulaiman
Website |  + postsBio
  • Abubakar Sulaiman
    Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe
  • Abubakar Sulaiman
    Ku Buɗe Wuta Kan Duk Wanda Kuka Gani Ɗauke Da Bindiga – IGP
  • Abubakar Sulaiman
    Ƴan Bindiga Sun Sace Shugaban Ƙaramar Hukumar Bungudu
  • Abubakar Sulaiman
    Obasanjo Da Atiku Sun Sake Musayar Zafafan Kalaman Zargin Juna

MASU ALAKA

Kwankwaso Zai Koma ADC Ranar Litinin
Manyan Labarai

2027: Magoya Bayan Tinubu Sun Yi Watsi Da Sukar Takarar Musulmi-Musulmi Da Kwankwaso Ya Yi

July 22, 2026
Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC
Labarai

Kabiru Gaya Ya Amince Zai Sauya Sheƙa Zuwa APC

July 21, 2026
Gwamnatin Tarayya Na Biyan Tallafin Man Fetur A Asirce – El-Rufai
Siyasa

Ba Zan Iya Jure Halayen El-Rufai Ba Shi Yasa Na Fice Daga ADC – Salihu Lukman

July 16, 2026
Next Post
Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki

LABARAI MASU NASABA

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

Rodri Ya Amince da Tayin Komawa Real Madrid

July 25, 2026
Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

Ministan Harkokin Wajen Sin Wang Yi Ya Yi Kira A Karfafa Hadin Gwiwa Na Kut-Da-Kut A SCO Domin Gina Duniya Mai Damawa Da Mabambantan Bangarori

July 25, 2026
Kalolin Kitso Na Zamani: Yadda Ake Yin Fulani Style

Muhimmancin Kula Da Gashi Domin Lafiyarsa Da Kyawunsa

July 25, 2026
Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

Kungiya Ta Nemi Mambobinta Su Rungumi Hanyoyin Kasuwanci Na Zamani

July 25, 2026
An Sanya Wuraren Sana’ar Kayan Tangaran Na Jingdezhen Cikin Jerin Wuraren Tarihi Na Duniya Na UNESCO

An Sanya Wuraren Sana’ar Kayan Tangaran Na Jingdezhen Cikin Jerin Wuraren Tarihi Na Duniya Na UNESCO

July 25, 2026
Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

Amfanin Ganyen Magarya Ga Lafiya Dan Adam

July 25, 2026
Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

Wane Ne Khalil Al-Hayya, Sabon Shugaban Kungiyar Hamas?

July 25, 2026
Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

Tsakanin Digiri Da Sana’a Wanne Ya Fi Muhimmanci A Wannan Lokacin?

July 25, 2026
PDP

Sojoji Sun Kamata Ƴan Bindiga 5 Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Mutane A Yobe

July 25, 2026
Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

Gwamnatin Jihar Kano Za Ta Fara Aiwatar Da Shirin Inshorar Lafiya Ga Jaruman Kannywood

July 25, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.