• English
  • Business News
Monday, August 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar Yaki Da Cizon Sauro: Majalisa Ta Bukaci Gwamnati Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Malaria

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Ranar Yaki Da Cizon Sauro: Majalisa Ta Bukaci Gwamnati Ta Ayyana Dokar Ta-baci Kan Malaria
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai ta tarayya ta bukaci gwamnatin tarayya ta ayyana dokar ta-baci kan cutar maleriya, tare da misalta cutar a matsayin mai mummuke mutane sannu a hankali da ke janyo mutuwan ‘yan Nijeriya.

Shugaban kwamitin yaki da cutar zazzabin cikin sauro, tarin fuka, da cutar nan mai karya garkuwar jiki wato (HIV), na majalisar, Hon. Amobi Ogah, shi ne ya shaida hakan ta cikin sanarwar da ya fitar ga ‘yan jarida a Abuja ranar Lahadi domin raya bikin ranar yaki da cizon sauro ta duniya na 2023.

  • Cutar Maleriya Ta Kashe Mutum 290,000 A Duniya A Cikin Shekara Biyu

Ana raya bikin yaki da cizon sauro ne a duk duniya a duk ranar 20 ga watan Agusta domin nazari da bibiyar hanyoyin dakile kisan da cizon sauro ke yi wa jama’a.

Manufar da ke cikin hakan shi ne domin wayar da kan jama’a da kuma daukan matakan kariya daga cutar tare da jawo hankalin hukumomi wajen daukan matakan da suka dace domin shawo kan cutar maleriya da ke addabar jama’a.

Ogah, dan majalisar mai wakiltar mazabar Isuiwuato/Umunneochi daga jihar Abia, ya ce, maleriya ta zama babban barazana ga kiwon lafiya, kuma akwai bukatar daukan dukkanin matakan dakile yawan mutuwa da ake yi a sanadiyyar cutar.

Labarai Masu Nasaba

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

Ya ce, majalisar ta 10 za ta yi dukkanin mai yiyu wajen ganin an rage kaifin illar da cutar maleriya ke yi a Nijeriya.

“Kwamitinmu za ta yi aiki da hukumomin da suka dace wajen yaki da cutar maleriya kuma za mu tabbatar dukanin kudin da aka ware an yi amfani da su domin tabbatar da cimma manufar da ake so.

“A cewar hukumar lafiya ta duniya, kasashen Afrika hudu sune ke da rinjayen masu mutuwa sakamakon cutar maleriya. Nijeriya kuma ita ce ke kan gaba da kaso 31.3 cikin dari, yayin da jamhuriyyar Congo take biye mata da kaso 12.6 cikin dari sai kuma, Tanzania mai kaso 4.1, yayin da jamhuriyyar Nijar take da kaso 3.9 cikin dari.”

Ya ce, Nijeriya na bukatar kariya daga cutar malaria. Ya bukaci gwamnati da masu ruwa da tsaki da su tabbatar sun rage kaifin yaduwar cutar maleriya tare da kare jama’a daga illar da zazzabin cizon sauro ke janyowa.

Dan majalisar ya ce dukkanin kokarin da ya dace a yi wajen kawar da cutar maleriya ya kamata a yi hakan domin kula da kiwon lafiyan al’ummar Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cizon sauroZazzabin Cizon Sauro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Sauya Wa Momoh, Oyetola, Alkali, Tunji-Ojo Ma’aikatu

Next Post

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

36 minutes ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

2 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

3 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

4 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

7 hours ago
Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta
Labarai

Sojoji Sun Kama Mutane 69 Masu Fasa Bututun Mai A Yankin Neja-Delta

11 hours ago
Next Post
Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

August 25, 2025
Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

Sin Ta Shiga Jerin Kasashe 3 Dake Sahun Gaba Wajen Gudanar Da Cinikayya Da Kasashe Da Yankunan Duniya 157

August 25, 2025
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

August 25, 2025
Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

Harin Asibitin Gaza Ya Halaka Mutane da Dama, Ciki Har da Ƴan Jarida

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.