ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Edo

Hukumar Gudanarwar Jami’ar Edo mallakin gwamnatin jihar, Ambrose Alli University (AAU), Ekpoma, ta kori ma’aikata guda biyar yayin da wasu 21 suke kan fuskantar bincike kan zargin aikata manyan laifuka daban-daban.

Mamba a kwamitin musamman (SIT), Austin Osakure, yayin da ke mika rahoton ayyukan SIT ga gwamna Godwin Obaseki a gidan gwamnati da ke Benin, ya shaida cewar ma’aikatan an koresu ne bisa la’akari da rahoton kwamitin da’a da ladaftarwa ta jami’ar.

  • Hazikan Daliban Kano Za Su Samu Gurbin Karatu Kyauta A Jami’ar CCU – Dakta Salwa

Osakure, ya bukaci gwamnatin Edo da ta kafa majalisar koli ta gudanarwar jami’ar AAU, tare da daukan manyan jami’ai na jami’ar, ya lura kan cewa zuwa yanzu ba a yabawa ko gamsuwa da ayyukan kwamitin SIT, sai ya ce, ko kuma a sabunta ko yin nazari kan dokokin jami’ar domin kyautata lamuranta.

ADVERTISEMENT

Ya shaida cewar jami’ar AAU ta bi umarnin gwamnatin jihar Edo wajen shiga cikin taimakekeniyar kiwon lafiya da ya fara aiki a ranar 1 ga watan Agustan 2023.

Mamban ya ce, “Dukkanin ma’aikatan jami’ar AAU da suke da sauran shekaru bakwai su kammala aiki an barsu ba su cikin shirin.

LABARAI MASU NASABA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

“Tsarin inshuran kiwon lafiya ta Edo na gudana yadda ya dace saboda ana biyan kudin ne kai tsaye ta asusun EdoHIS, domin tabbatar da gaskiya da adalci.

“Dalibai 998 sun shiga shirin, da sama da naira miliyan 15, da kuma ma’aikata 1,800 da sama da naira miliyan 31.

“Jami’ar ta gano kesa-kesai sama da 30 na dalibai ‘yan kasashen waje a cikin shekaru kasa da biyu, sun zana jarabawa har ma an yayesu. Ma’aikata da shugabannin tsangayoyin da suke da hannu a wannan lamarin an mika su ga jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da ICPC domin daukan mataki na gaba.”

Mamban ya bayyana wa gwamnan cewar akwai tsare-tsare da dama wadanda suke tafiya a jami’ar da suke bukatar gaggawan kawo dauki da sauyi domin bunkasa harkokin jami’ar.

A jawabinsa, gwamnan jihar, Godwin Obaseki, ya ce, gwamnatinsa za ta tabbatar da dawo da martaba da kimar jami’ar AAU, kuma nan kusa za a samu sauye-sauye masu matukar fa’ida.

Obaseki ya ce, “Muna son mu magance matsalolin makarantar,” ya tabbatar.

Edo
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Next Post
Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.