ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Edo

Hukumar Gudanarwar Jami’ar Edo mallakin gwamnatin jihar, Ambrose Alli University (AAU), Ekpoma, ta kori ma’aikata guda biyar yayin da wasu 21 suke kan fuskantar bincike kan zargin aikata manyan laifuka daban-daban.

Mamba a kwamitin musamman (SIT), Austin Osakure, yayin da ke mika rahoton ayyukan SIT ga gwamna Godwin Obaseki a gidan gwamnati da ke Benin, ya shaida cewar ma’aikatan an koresu ne bisa la’akari da rahoton kwamitin da’a da ladaftarwa ta jami’ar.

  • Hazikan Daliban Kano Za Su Samu Gurbin Karatu Kyauta A Jami’ar CCU – Dakta Salwa

Osakure, ya bukaci gwamnatin Edo da ta kafa majalisar koli ta gudanarwar jami’ar AAU, tare da daukan manyan jami’ai na jami’ar, ya lura kan cewa zuwa yanzu ba a yabawa ko gamsuwa da ayyukan kwamitin SIT, sai ya ce, ko kuma a sabunta ko yin nazari kan dokokin jami’ar domin kyautata lamuranta.

ADVERTISEMENT

Ya shaida cewar jami’ar AAU ta bi umarnin gwamnatin jihar Edo wajen shiga cikin taimakekeniyar kiwon lafiya da ya fara aiki a ranar 1 ga watan Agustan 2023.

Mamban ya ce, “Dukkanin ma’aikatan jami’ar AAU da suke da sauran shekaru bakwai su kammala aiki an barsu ba su cikin shirin.

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

“Tsarin inshuran kiwon lafiya ta Edo na gudana yadda ya dace saboda ana biyan kudin ne kai tsaye ta asusun EdoHIS, domin tabbatar da gaskiya da adalci.

“Dalibai 998 sun shiga shirin, da sama da naira miliyan 15, da kuma ma’aikata 1,800 da sama da naira miliyan 31.

“Jami’ar ta gano kesa-kesai sama da 30 na dalibai ‘yan kasashen waje a cikin shekaru kasa da biyu, sun zana jarabawa har ma an yayesu. Ma’aikata da shugabannin tsangayoyin da suke da hannu a wannan lamarin an mika su ga jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da ICPC domin daukan mataki na gaba.”

Mamban ya bayyana wa gwamnan cewar akwai tsare-tsare da dama wadanda suke tafiya a jami’ar da suke bukatar gaggawan kawo dauki da sauyi domin bunkasa harkokin jami’ar.

A jawabinsa, gwamnan jihar, Godwin Obaseki, ya ce, gwamnatinsa za ta tabbatar da dawo da martaba da kimar jami’ar AAU, kuma nan kusa za a samu sauye-sauye masu matukar fa’ida.

Obaseki ya ce, “Muna son mu magance matsalolin makarantar,” ya tabbatar.

Edo
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    M.A. Abubakar Ya Zaɓi Farouk Mustapha A Matsayin Mataimakinsa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu

MASU ALAKA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau
Rahotonni

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano
Labarai

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi
Labarai

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
Next Post
Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

Wasu Sassan Birnin Abuja Na Fuskantar Barazanar Rusau

July 17, 2026
Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.