ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Jami’ar Edo Ta Kori Ma’aikata 5, Wasu 21 Na Fuskantar Bincike Kan Aikata Manyan Laifuka

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Edo

Hukumar Gudanarwar Jami’ar Edo mallakin gwamnatin jihar, Ambrose Alli University (AAU), Ekpoma, ta kori ma’aikata guda biyar yayin da wasu 21 suke kan fuskantar bincike kan zargin aikata manyan laifuka daban-daban.

Mamba a kwamitin musamman (SIT), Austin Osakure, yayin da ke mika rahoton ayyukan SIT ga gwamna Godwin Obaseki a gidan gwamnati da ke Benin, ya shaida cewar ma’aikatan an koresu ne bisa la’akari da rahoton kwamitin da’a da ladaftarwa ta jami’ar.

  • Hazikan Daliban Kano Za Su Samu Gurbin Karatu Kyauta A Jami’ar CCU – Dakta Salwa

Osakure, ya bukaci gwamnatin Edo da ta kafa majalisar koli ta gudanarwar jami’ar AAU, tare da daukan manyan jami’ai na jami’ar, ya lura kan cewa zuwa yanzu ba a yabawa ko gamsuwa da ayyukan kwamitin SIT, sai ya ce, ko kuma a sabunta ko yin nazari kan dokokin jami’ar domin kyautata lamuranta.

ADVERTISEMENT

Ya shaida cewar jami’ar AAU ta bi umarnin gwamnatin jihar Edo wajen shiga cikin taimakekeniyar kiwon lafiya da ya fara aiki a ranar 1 ga watan Agustan 2023.

Mamban ya ce, “Dukkanin ma’aikatan jami’ar AAU da suke da sauran shekaru bakwai su kammala aiki an barsu ba su cikin shirin.

LABARAI MASU NASABA

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

“Tsarin inshuran kiwon lafiya ta Edo na gudana yadda ya dace saboda ana biyan kudin ne kai tsaye ta asusun EdoHIS, domin tabbatar da gaskiya da adalci.

“Dalibai 998 sun shiga shirin, da sama da naira miliyan 15, da kuma ma’aikata 1,800 da sama da naira miliyan 31.

“Jami’ar ta gano kesa-kesai sama da 30 na dalibai ‘yan kasashen waje a cikin shekaru kasa da biyu, sun zana jarabawa har ma an yayesu. Ma’aikata da shugabannin tsangayoyin da suke da hannu a wannan lamarin an mika su ga jami’an hukumar tsaro ta farin kaya DSS da ICPC domin daukan mataki na gaba.”

Mamban ya bayyana wa gwamnan cewar akwai tsare-tsare da dama wadanda suke tafiya a jami’ar da suke bukatar gaggawan kawo dauki da sauyi domin bunkasa harkokin jami’ar.

A jawabinsa, gwamnan jihar, Godwin Obaseki, ya ce, gwamnatinsa za ta tabbatar da dawo da martaba da kimar jami’ar AAU, kuma nan kusa za a samu sauye-sauye masu matukar fa’ida.

Obaseki ya ce, “Muna son mu magance matsalolin makarantar,” ya tabbatar.

Edo
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18
Labarai

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026
Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura
Rahotonni

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari
Labarai

Sanata Yari Ya Gudanar Da Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

September 12, 2026
Next Post
Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

Dandalin Kafofin Watsa Labarai Na BRICS Karo Na 6 Ya Yi Kira Da A Karfafa Muryoyin Kasashe Masu Tasowa

LABARAI MASU NASABA

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026
Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Sanata Yari Ya Gudanar Da Taron Masu Ruwa Da Tsaki A Zamfara

September 12, 2026
Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

Gwamna Dauda Lawal Ya Raba Motocin Aiki Ga Manyan Makarantu A Zamfara

September 12, 2026
Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

Dangote Ya Ƙara Farashin Fetur, Kwana 2 Kafin Shiga Kasuwar Hannun jari

September 12, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Jam’iyyar APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Shugaban Ƙasa Da Gwamnoni A Nijeriya -Dikko Raɗɗa

September 12, 2026
NNPCL Ya Rage Farashin Man Fetur Zuwa ₦860 Kan Kowacce Lita – IPMAN

Mene Ne Ra’ayinku Kan Dawo Da Tallafin Man Fetur Ko Barin Sa?

September 12, 2026
Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

Sin Ta Nuna Rashin Jin Dadinta Ga Italiya Da Tarayyar Turai Kan Ziyarar Jami’ar DPP

September 11, 2026
Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

Sin Tana Son Cin Moriya Tare Da Sassan Duniya A Fannin Kirkire-kirkire

September 11, 2026
Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

Sin Da Indiya Na Shirye-shiryen Ganawar Xi Da Modi

September 11, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.