• English
  • Business News
Tuesday, October 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya: An Yi Wa Malamar Jinya Daurin Rai Da Rai Bisa Laifin Kashe Jarirai

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Malamar jinya

An yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga wata ma’aikaciyar jinyar jarirai, Lucy Letby, wadda ita ce ta fi yi wa kananan yara kisan dauki dai-dai a tarihin baya-bayan nan na Birtaniya.

An yanke mata hukunci ne bayan samun ta da laifin kashe jarirai bakwai, da kuma yunkurin kashe karin shida a wani asibitin yara da ke Countess of Chester.

  • Ingila Ta Rage Haraji Kan Kayayyakin Nijeriya 3,000

Da gangan, Lucy Letby ta rika yi wa jarirai allura da sauran iska a cikin sirinji, kuma ta rika yi wa wasu dura da karfi, sannan ta bai wa jarirai biyu guba da sinadarin insulin.

Bayan yanke mata wannan hukunci, Lucy Letby ba ta nuna wata alamar nadama ba.

A yazu dai Letby za ta shafe tsawon gaba dayan rayuwarta a tsare, inda ta zama mace ta hudu a Birtaniya da aka taba yankewa irin wannan hukunci, wanda shi ne mafi tsanani da ake yankewa mai laifi.

LABARAI MASU NASABA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Alkalin kotun Mai shari’a Goss, ya bayyana laifin da Lucy ta aikata a matsayin “babban abin kyama”.

Ya ce “ta aikata abin da ya saba da tunanin dan’adam mai cikakken hankali, da ya san kimar lura da jarirai, kuma babbar cin amanar wadanda suka yarda da aikin ma’aikatan lafiya ne”.

Alkalin ya bayyana ta a matsayin mara tausayi, wadda ke sanya damuwarta cikin aikinta.

Lauyan da ke kare ta, Ben Myers KC, ya ce “Tun bayan fara shari’ar Lucy ta ki musanta aikata laifin da ake zargin ta da aikatawa, dangane haka ba shi da wani mataki da zai dauka da zai iya kai wa ga rage tsawon hukuncin da aka yanke mata”.

Harabar kotun ta cika makil da iyayen yaran da ma’aikaciyar jinyar ta halaka wa jarirai, har ma wasu sun yi sharbar hawaye a lokacin da alkalin yake karanta hukuncin da ya yanke wa mai laifin.

An ga wasu daga cikin masu sauraron karar rai a bace lokacin da suka saurari bayanan alkalin.

Wata uwa da ita ma, ta rasa danta ta ce “akwai takaici a ce akwai mutumin da zai iya aikata irin wannan mummunar aika-aika”.

Ita ma wata mahaifiya da aka kashe jaririnta cike da bakin ciki, ta sanar da kotun cewa, “ Game da mutuwar danta, tana ganin lamarin kamar a cikin wani fim din ban tsoro”.

Haka zalika, wata uwa da ke rungume da zomon wasa na yara, ta sanar da kotun cewa “Abin da Lucy Letby ta aikata, mugunta ce da kuma babban abin kunya ne sakaci a matsayinta na malamar jinya da aka bai wa amana”.

Su ma iyayen wata jaririya da aka bayyana sunanta da Baby G, wadda ita ce bakwaini mafi kankanta a cikin dukkan jariran, wacce nauyinta bai fi giram 535, sun fada wa kotun cewa: “Allah ya raya ta” amma sai “ta fada hannun shaidanu”.

Kimanin mutum 70 ne aka taba yankewa irin wannan hukunci na daurin rai-da-rai, inda ake ci gaba da duba lafiyar kwakwalwar hudu a asibiti. Idan aka yanke irin wannan hukunci, ba a taba sauya shi ba, sai dai bisa wasu dalilai na ba sabon ba.

Sauran matan da aka taba yankewa irin wannan hukunci sakamakon yi wa mutane kisan dauki dai-dai, akwai Rose West da Joanna Dennehy, sai kuma Myra Hindley, wadda tun a wancan lokacin ta riga mu gidan gaskiya.

Jagoran jam’iyyar adawa ta Labour, Keir Starmer, ya yi kira ga gwamnati ta tilasta wa masu laifin da ake yanke wa hukunci su rika fuskantar wadanda aka aikata wa laifi, ganin Letby ta ki bayyana a gaban kotu lokacin da aka yanke mata hukunci.

Ya ce “Ina son ganin an dauki mataki cikin gaggawa a wannan shari’a, saboda iyayen wadanda lamarin ya shafa sun shiga mummunar damuwa.

“Muna neman a samar da sauyi a doka wanda zai tilasta wa masu laifi, su saurari hukuncin da ake yanke musu”, in ji shi.

Shi ma Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak, ya ce gazawa ce da kuma tsoro a ce wadanda aka yanke wa hukunci a cikin kotu, su ki fuskantar iyalan da suka aikata wa laifi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole
Labarai

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU
Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara
Manyan Labarai

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
Next Post
Nijeriya Na Asarar Gangar Danyen Mai 400,000 A Kullum – NSA

Nijeriya Na Asarar Gangar Danyen Mai 400,000 A Kullum – NSA

LABARAI MASU NASABA

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

Matsayar Kasar Sin A Bayyane Take Dangane Da Batutuwan Cinikayya Da Tsagin Amurka

October 20, 2025
An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

An Shiga Ruɗani A Borno Bayan Budurwa Ta Kashe Kanta Saboda Auren Dole

October 20, 2025
Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

Sin Ta Kara Wasu Wurare 22 Cikin Yankunan Dausayi Masu Matukar Muhimmanci A Kasar

October 20, 2025
Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

Tinubu Ya Taya Kwankwaso Murnar Ranar Haihuwa, Ya Jaddada Abotarsu

October 20, 2025
Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

Sin Ta Yi Maraba Da Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Afghanistan

October 20, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Bai Wa Gwamnatin Tarayya Wa’adin Mako 4 Ta Sasanta Da ASUU

October 20, 2025
Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira

October 20, 2025
Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

Mutane 3,433 Sun Rasa Rayukansu A Haɗurra 6,858 A Cikin Watanni Tara

October 20, 2025
An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.