• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Alamun Japan Ta Debo Ruwan Dafa Kanta

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Japan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun a ranar 24 ga wannan wata ne, kasar Japan ta fara sakin ruwan dagwalon tashar nukiliyar Fukushima zuwa cikin teku, lamarin da ya gamu da rashin amincewa daga bangarori da dama daga ciki da wajen kasar. Sanin kowa ne cewa, batun amincewa da shirin Japan na zubar da ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku, ba batu ne da wasu kasashe tsiraru za su amincewa ba, musamman karkashin bukatun kasashe na cimma burin siyasa.

A shekarar 2021 ne dai Japan ta bijiro da wannan aniya, bayan da wata girgizar kasar ranar 11 ga watan Maris din a shekarar 2011 da ta lalata tashar nukiliyar Fukushima, tare da haddasa yoyon sinadarin nukiliya, tun lokacin ne kuma aka rika nusar da Japan da ma wadanda suka bayar da shawarar aikata wannan danyen aiki.

  • Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

Idan ba a manta ba, shi ma taron kasashen nan 7 masu karfin tattalin arziki a duniya wato G7 da ya gudana a kasar ta Japan, bai goyi bayan shirin kasar na zubar da ruwan dagwalon a cikin teku ba, saboda illarsa ga yanayin teku da tsaron abinci da ma lafiyar daukacin bil-Adama, amma bangaren Japan ya ci gaba da yin kunnen uwar shegu da neman kare kansa ta kowace hanya, wai don saboda arahar wannan tsari, wanda masu iya magana ke cewa, ba ta ado.

Abin takaici shi ne, yadda Japan ta dage cewa, wai shirin nata ya samu amincewar Amurka, da wasu karin kasashen ma yaudarar kai ne kawai, saboda wannan danyen aiki zai shafi lafiyar al’ummar duniya ne baki daya.

Ya kamata Japan ta fahimci cewa, akwai kasashe kusan 200 a duniya, kuma kalilan ne suka bayyana amincewa da shirin nata. Hasali ma dai mafi yawan kasashen duniya ciki har da al’ummar Japan da kansu, sun bayyana adawa, da rashin gamsuwa da zubar da ruwan dagwalon nukiliyar cikin teku.

Labarai Masu Nasaba

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Gaskiyar al’amari shi ne bai kamata Japan ta kawar da kai daga gaskiya ba, balle kuma ta rika yaudarar kanta”. Wannan ya kara nuna cewa, Japan ba ta damu da lafiyar jama’arta ba, balle ma ta damu da lafiyar al’ummar duniya. Abin dake tabbatar da cewa, Japan ta debo ruwan dafa kanta da kanta.

Yanzu dai kasar Sin ta dauki matakin kare lafiyar jama’arta da ma na ragowar kasashen duniya, ta hanyar haramta shigo da kayan ruwa daga Japan, tun lokacin da Japan din ta fara sakin ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku.

Masharhanta na cewa, zubar da ruwan dagwalon nukiliyar da Japan ta yi, ko shakka babu zai shafi muhallin teku da lafiyar bil adama. Kuma mataki ne na nuna karfin iko, da yin watsi da damuwar sassan kasa da kasa, da martaba moriyar kai, da yin fatali da moriyar sauran sassan kasa da kasa. Amma kowa ya debo da zafi aka ce bakinsa.

Sai dai a maimakon gyara kuskuren da ya yi, bangaren Japan ya rika nuna yatsa ga kasar Sin. Kafofin yada labaran kasar Japan da dama sun yi ta yayata zargin da ake yi na cewa, kiyayyar Japanawa a kasar Sin na kara zafafa, kuma Sinawa na daukar matakan “tsana” kan kasar Japan. Firaministan Japan Fumio Kishida da wasu ‘yan siyasar kasar da dama, sun bukaci kasar Sin da ta soke takunkumin hana shigo da kayayyakin ruwa na Japan, har ma sun yi barazanar daukar matakai kan wannan lamari.

Wannan wani bangare ne na yakin “ra’ayin jama’a” da Japan ta shirya a hankali. A ranar da Japan din ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, a cewar kafar watsa labarai ta kasar Japan NHK, ma’aikatar harkokin wajen Japan ta tsara manufar daidaita abin da aka kira “labaran karya”, yawan kudin da ta ware domin aiwatar da manufar ya kai kusan JPY biliyan 70. Idan aka duba rahoton daidaita ruwan dagwalon nukiliya da Japan ta fitar a shekarar 2020, yawan kudin da Japan ta ware wajen daidaita labaran karya, ya fi kasafin kudin zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku yawa har sau 20.

Ana iya ganin cewa, bangaren Japan ya zabi zubar da ruwan dagwalon nukiliya zuwa teku don tsimin kudi, amma ya kashe kudi da yawa don kawata shi. An yi nuni da cewa, bangaren Japan yana zargin Sin yana dora wa kasar Sin laifi ne, domin rikitar da ra’ayin jama’a da kuma mayar da kanta a matsayin “wadda aka raunata”, ta boye abin da ta yi na gurbata muhalli da kuma illata lafiyar bil Adama, a yunkurin rage zargin da ake yi mata dangane da batun zubar da ruwan dagwalon nukiliya zuwa teku. (Ibrahim Yaya, Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Tottenham Da Chelsea Na Zawarcin Ansu Fati Na Barcelona

Next Post

Gidajen Wanka Sun Kara Kudin Ba-Haya A Kano

Related

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu
Daga Birnin Sin

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

16 hours ago
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili
Daga Birnin Sin

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

18 hours ago
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

18 hours ago
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya
Daga Birnin Sin

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

22 hours ago
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

24 hours ago
Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Na Ganin Tattaunawa Da Hadin Gwiwa A Matsayin Hanyar Warware Takaddamar Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka

1 day ago
Next Post
Gidajen Wanka Sun Kara Kudin Ba-Haya A Kano

Gidajen Wanka Sun Kara Kudin Ba-Haya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.