ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Alamun Japan Ta Debo Ruwan Dafa Kanta

by CMG Hausa
3 years ago
Japan

Tun a ranar 24 ga wannan wata ne, kasar Japan ta fara sakin ruwan dagwalon tashar nukiliyar Fukushima zuwa cikin teku, lamarin da ya gamu da rashin amincewa daga bangarori da dama daga ciki da wajen kasar. Sanin kowa ne cewa, batun amincewa da shirin Japan na zubar da ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku, ba batu ne da wasu kasashe tsiraru za su amincewa ba, musamman karkashin bukatun kasashe na cimma burin siyasa.

A shekarar 2021 ne dai Japan ta bijiro da wannan aniya, bayan da wata girgizar kasar ranar 11 ga watan Maris din a shekarar 2011 da ta lalata tashar nukiliyar Fukushima, tare da haddasa yoyon sinadarin nukiliya, tun lokacin ne kuma aka rika nusar da Japan da ma wadanda suka bayar da shawarar aikata wannan danyen aiki.

  • Kasashen Dake Kewayen Tekun Pasifik Suna Da Ikon Neman Diyya Daga Gwamnatin Japan Kan Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ruwa Cikin Teku

Idan ba a manta ba, shi ma taron kasashen nan 7 masu karfin tattalin arziki a duniya wato G7 da ya gudana a kasar ta Japan, bai goyi bayan shirin kasar na zubar da ruwan dagwalon a cikin teku ba, saboda illarsa ga yanayin teku da tsaron abinci da ma lafiyar daukacin bil-Adama, amma bangaren Japan ya ci gaba da yin kunnen uwar shegu da neman kare kansa ta kowace hanya, wai don saboda arahar wannan tsari, wanda masu iya magana ke cewa, ba ta ado.

ADVERTISEMENT

Abin takaici shi ne, yadda Japan ta dage cewa, wai shirin nata ya samu amincewar Amurka, da wasu karin kasashen ma yaudarar kai ne kawai, saboda wannan danyen aiki zai shafi lafiyar al’ummar duniya ne baki daya.

Ya kamata Japan ta fahimci cewa, akwai kasashe kusan 200 a duniya, kuma kalilan ne suka bayyana amincewa da shirin nata. Hasali ma dai mafi yawan kasashen duniya ciki har da al’ummar Japan da kansu, sun bayyana adawa, da rashin gamsuwa da zubar da ruwan dagwalon nukiliyar cikin teku.

LABARAI MASU NASABA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

Gaskiyar al’amari shi ne bai kamata Japan ta kawar da kai daga gaskiya ba, balle kuma ta rika yaudarar kanta”. Wannan ya kara nuna cewa, Japan ba ta damu da lafiyar jama’arta ba, balle ma ta damu da lafiyar al’ummar duniya. Abin dake tabbatar da cewa, Japan ta debo ruwan dafa kanta da kanta.

Yanzu dai kasar Sin ta dauki matakin kare lafiyar jama’arta da ma na ragowar kasashen duniya, ta hanyar haramta shigo da kayan ruwa daga Japan, tun lokacin da Japan din ta fara sakin ruwan dagwalon nukiliyar a cikin teku.

Masharhanta na cewa, zubar da ruwan dagwalon nukiliyar da Japan ta yi, ko shakka babu zai shafi muhallin teku da lafiyar bil adama. Kuma mataki ne na nuna karfin iko, da yin watsi da damuwar sassan kasa da kasa, da martaba moriyar kai, da yin fatali da moriyar sauran sassan kasa da kasa. Amma kowa ya debo da zafi aka ce bakinsa.

Sai dai a maimakon gyara kuskuren da ya yi, bangaren Japan ya rika nuna yatsa ga kasar Sin. Kafofin yada labaran kasar Japan da dama sun yi ta yayata zargin da ake yi na cewa, kiyayyar Japanawa a kasar Sin na kara zafafa, kuma Sinawa na daukar matakan “tsana” kan kasar Japan. Firaministan Japan Fumio Kishida da wasu ‘yan siyasar kasar da dama, sun bukaci kasar Sin da ta soke takunkumin hana shigo da kayayyakin ruwa na Japan, har ma sun yi barazanar daukar matakai kan wannan lamari.

Wannan wani bangare ne na yakin “ra’ayin jama’a” da Japan ta shirya a hankali. A ranar da Japan din ta fara zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku, a cewar kafar watsa labarai ta kasar Japan NHK, ma’aikatar harkokin wajen Japan ta tsara manufar daidaita abin da aka kira “labaran karya”, yawan kudin da ta ware domin aiwatar da manufar ya kai kusan JPY biliyan 70. Idan aka duba rahoton daidaita ruwan dagwalon nukiliya da Japan ta fitar a shekarar 2020, yawan kudin da Japan ta ware wajen daidaita labaran karya, ya fi kasafin kudin zubar da ruwan dagwalon nukiliya cikin teku yawa har sau 20.

Ana iya ganin cewa, bangaren Japan ya zabi zubar da ruwan dagwalon nukiliya zuwa teku don tsimin kudi, amma ya kashe kudi da yawa don kawata shi. An yi nuni da cewa, bangaren Japan yana zargin Sin yana dora wa kasar Sin laifi ne, domin rikitar da ra’ayin jama’a da kuma mayar da kanta a matsayin “wadda aka raunata”, ta boye abin da ta yi na gurbata muhalli da kuma illata lafiyar bil Adama, a yunkurin rage zargin da ake yi mata dangane da batun zubar da ruwan dagwalon nukiliya zuwa teku. (Ibrahim Yaya, Safiyah Ma)

Japan
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines
Daga Birnin Sin

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ya Soki Dabarar Siyasa Ta Sakataren Tsaron Philippines

June 12, 2026
Next Post
Gidajen Wanka Sun Kara Kudin Ba-Haya A Kano

Gidajen Wanka Sun Kara Kudin Ba-Haya A Kano

LABARAI MASU NASABA

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026
Yawan Man Da Nijeriya Ke Hakowa Ya Karu Da Ganga 177,000 A Janairu

Dalilin Da Ya Sa Matatar Dangote Ta Kara Habaka Tura Man Fetur

June 13, 2026
Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

Zan Saki Nnamdi Kanu Idan Na Zama Shugaban Ƙasa – Peter Obi

June 13, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

NPA Da Birtaniya Sun Kulla Yarjejeniyar Zamanantar Da Tashoshin Jiragen Ruwan Nijeriya

June 13, 2026
Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

Sukar Da Ake Yi Wa Mbappé Ta Yi Yawa — Dembélé

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.