• English
  • Business News
Friday, May 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Wannan Hadin Gwiwa Na Taimakawa Kokarin Tinkarar Sauyawar Yanayi A Afirka

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sauyawar yanayin duniya na samar da mummunan tasiri kan muhallin halittu, da tattalin arziki, gami da zaman al’umma a nahiyar Afirka.

An ce a bana akwai mutane ‘yan Afirka kimanin miliyan 1.8 da fari ya tilasta musu bari muhallinsu. Yayin da aka samu mummunar ambaliyar ruwa a kasar Jamhuriyar Dimokuradiyyar Congo, kana mahaukaciyar guguwa da ake kira Freddy ta haddasa babbar asara a kasashen Malawi da Mozambique.

  • Yaushe Japan Za Ta Kawo Karshen Laifinta?

An ce, sakamakon karuwar zafin yanayi a kai a kai, bala’o’i daban daban za su iya yin mummunan tasiri mafi tsanani a nan gaba.

Sai dai, ban da jure wahalhalun da matsalar sauyawar yanayi ke haifarwa, kasashen Afirka za su iya taka muhimmiyar rawa a kokarin daidaita wannan matsala.

Hakika dimbin albarkatun da nahiyar Afirka ke da su, da matasa masu tarin yawa da al’ummun nahiyar ta kunsa, suna samar da damammaki ga yunkurin sauya salon ci gaban tattalin arzikin kasashen Afirka da na duniya zuwa irin na kare muhalli, da neman raya tattalin arziki ba tare da fitar da iska mai dumama yanayi mai yawa ba.

Labarai Masu Nasaba

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

Kana burin raya tattalin arzikin nahiyar ba tare da haddasa dumamar yanayi ba wani muhimmin batu da ke daukar hankalin mahalarta taron koli na Afirka na tinkarar sauyawar yanayin duniya na farko, da aka kaddamar da shi yau a kasar Kenya.

Ana sa ran ganin gwamnatocin kasashen Afirka za su tsara wata taswirar raya tattalin arziki ba tare da haddasa dumamar yanayi ba a nahiyar Afirka, a wajen taron na wannan karo. Har ila yau, kasashen Afirka za su yi amfani da wannan dama wajen ingiza hadin gwiwar da suke yi tare da abokan hulda na kasashe daban daban, a kokarin tinkarar sauyawar yanayi. Kana hadin gwiwar da suke yi tare da kasar Sin ta riga ta zama wani misali mai kyau a wannan fanni.

Tun daga shekarar 2000, kasashen Afirka da kasar Sin sun jaddada bukatar karfafa hadin giwarsu a fannin kare muhalli, yayin taron ministoci na farko karkashin laimar dandalin hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin (FOCAC). Zuwa yanzu, a karkashin wannan laima, kasar Sin ta riga ta gudanar da wasu ayyuka fiye da dari na samar da makamashi mai tsabta, da samun ci gaban tattalin arziki tare da kare muhalli a lokaci guda, wadanda suka kunshi kafa yankin misali na rage hayaki mai dumama yanayi, da yankin misali na tinkarar sauyawar yanayi a nahiyar Afirka, da taimakawa kasashen Afirka gina “shingen kare kwararowar hamada”, da dai sauransu.

Don neman samun ci gaban tattalin arizki ta wata hanyar da ta dace da ra’ayi na kare muhalli, dole ne a yi kokarin samar da makamashi mai tsabta, wanda ba zai haddasa dumamar yanayi ba. A wannan fanni, hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin ta samarwa nahiyar Afirka da dimbin manyan ayyuka.

A kasar Afirka ta Kudu, tashar samar da wutar lantarki ta karfin iska ta garin De Aar, wadda wani kamfanin Sin ya gina, ta fara samar da wutar lantarki a shekarar 2017, ta yadda aka samu damar saukaka yanayin kunci da kasar ta Afirka ta Kudu ke ciki na karancin wutar lantarki.

Kana a kasar Kenya, tashar samar da makamashi da hasken rana ta Garissa, mafi girma a yankin gabashin Afirka, wadda wani kamfanin kasar Sin ya gina, ita ma ta fara aiki a shekarar 2019.

Inda wutar lantarki da take samarwa za ta iya biyan bukatun iyalai dubu 70, kwatankwacin mutane fiye da dubu 380. Yayin da a kasar Najeriya, tashar samar da wutar lantarki ta karfin ruwa ta Zungeru, da wani kamfanin Sin ya gina, tana samar da karin wutar lantarki ta 2.64 billion kWh ga jama’ar kasar a kowace shekara.

Ban da samar da wasu manyan ayyuka, fasahohi na kasar Sin su ma suna taka rawar gani a kokarin raya tattalin arzikin kasashen Afirka gami da magance fitar da iska mai dumama yanayi a lokaci guda.

A watan Maris na bara, kamfanin BasiGo na kasar Kenya ya zama na farko a kasar, a fannin aikin hada manyan motoci na bas masu amfani da wutar lantarki.

Wannan kamfani yana yin amfani da na’urori da kayayyaki da kamfanin BYD na kasar Sin ya samar, wajen hada motocin bas a kasar Kenya. A cewar wani babban darekta na kamfanin, yadda kamfanin na kasar Sin ke raba fasahohi tare da su ya ba kamfanin Basigo damar raya harkoki cikin matukar sauri, ba tare da shan wahalhalu a mataki na farko na sana’ar ba.

Kana a kasar Rwanda, an taba gamuwa da matsalar gina madatsar ruwa kan tushen wani fili mai taushi, yayin da ake gina wata madatsar ruwa kan kogin Nabarronge. Daga baya dimbin cibiyoyin nazarin fasahohi na kasar Sin sun taimaka wajen daidaita wannan matsala, inda suka samar da wata dabara, ta yadda ake iya ci gaba da gudanar da aikin gina madatsar ruwan.

Ta hanyar duba sakamakon da aka samu ta hanyar gudanar da hadin gwiwa tsakanin kasashen Afirka da kasar Sin a fannin raya tattalin arziki ba tare da samun dumamar yanayi ba, za mu iya ganin cewa an lura da hakikanan bukatun da kasashen Afirka ke da su, da kokarin taimaka musu daidaita matsaloli. Kana an samar da sauki sosai ga yunkurin yin hadin gwiwa ta hanyoyi daban daban, da yadda ake mika fasahohi. Zuwa yanzu, hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin na taka muhimmiyar rawa a fannin sauya tsarin raya tattalin arziki ta kasashen Afirka zuwa wani nau’i na kare muhalli, da tabbatar da ci gaban kasashen ba tare da samar da iska mai dumama yanayi sosai ba.

A sa’i daya kuma, ana samar da misalai ga sauran kasashe, kan yadda za su iya gudanar da hadin gwiwa tare da kasashen Afirka.

Sa’an nan taron kolin da aka kaddamar da shi a kasar Kenya a wannan karo zai zame wa kasashen Afirka wata kyakkyawar dama ta kara yin hadin kai tare da sauran kasashe, a fannin neman ci gaba ba tare da samar da iska mai dumama yanayi sosai ba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shugabancin Kasa: Kotu Za Ta Yanke Hukunci A Ranar Laraba

Next Post

Gwamna Uba Sani Ya Amince A Biya Likitoci Kashi 100 Na Sabon Tsarin Albashinsu

Related

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

31 minutes ago
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

2 hours ago
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu
Daga Birnin Sin

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

3 hours ago
An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 
Daga Birnin Sin

An Gudanar Da Dandalin Kawancen Birane Na Kasa Da Kasa Na Shanghai 

22 hours ago
Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600
Daga Birnin Sin

Darajar Sashen Masana’antun AI Na Sin Ta Kai Kusan Yuan Biliyan 600

22 hours ago
Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda
Daga Birnin Sin

Sanarwar Bayan Taron Kolin Sin Da ASEAN Da GCC Ta Yi Nuni Ga Burin Kara Dunkulewa Waje Guda

1 day ago
Next Post
Gwamna Uba Sani Ya Sake Nadin Sabbin Mukamai A Jihar Kaduna 

Gwamna Uba Sani Ya Amince A Biya Likitoci Kashi 100 Na Sabon Tsarin Albashinsu

LABARAI MASU NASABA

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar

May 30, 2025
Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

Kudin Shigar Masana’antar Manhajojin Sin Ya Karu Da 10.8% A Watanni Hudu Na Farkon Bana

May 30, 2025
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

May 30, 2025
An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

An Yi Bikin Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Kafa Hukumar Shiga Tsakani Ta Kasa Da Kasa A Hong Kong Na Kasar Sin

May 30, 2025
Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

Sulhun PDP Ya Haɗu Da Cikas, Wike Ya Janye Daga Duk Wata Yarjejeniya

May 30, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Tattaunawa Ta Hudu Kan Musaya Da Koyi Da Juna A Tsakanin Al’ummomi Ta Fannin Wayewar Kansu

May 30, 2025
Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

Tinubu Ya Sanya Hannu Kan Dokar Rage Farashin Mai Da Iskar Gas

May 30, 2025
Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto

Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 60 A Borno

May 30, 2025
Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

Kotun Ɗaukaka Ƙara Ta Tabbatar Da Zaɓen Ƙananan Hukumomin Kano

May 30, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 30-03-2025

May 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.