ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Kasa: Kotu Za Ta Yanke Hukunci A Ranar Laraba

Atiku, Obi Da Tinubu Za Su San Matsayarsu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotu
  •  Za A Yada Hukuncin Kai Tsaye A Gidajen Talebijin

Kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa na zaben 2023 da ya gudana, za ta yanke hukuncinta a ranar Laraba 6 ga watan Satumba kan korafe-korafen da aka shigar da ke kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu. 

 

Hukuncin da za ta yanke kan karar da jam’iyyar LP da dan takararta Peter Obi da PDP da dan takararta Atiku Abubakar da  APM da suka shigar suna kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu (APC) a matsayin shugaban Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Umarci Jakadun Nijeriya Da Su Dawo Gida

A wata sanarwar da rijistan kotun daukaka kara Umar M. Bangari Esq ya fitar a ranar Litinin, ya ce wadanda aka tantance ne kawai za su samu shiga cikin kwaryar kotun.

 

LABARAI MASU NASABA

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Ya kuma ce domin tabbatar da gaskiya da yin komai a bayyane, za a yada zaman hukuncin kai tsaye a gidajen talebijin na kasa domin al’umma su bibiya kai tsaye.

 

Sanarwar ta ce, “Kotun daukaka kara tana sanar da al’umma cewa za a yanke hukunci kan kararrakin da aka gabatar a gaban kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa a ranar Laraba 6 ga watan Satumba, 2023.

 

Hukunci tsakanin “• CAREPC/03/2023 tsakanin Mr. Peter Gregory Obi & Anor tsakani da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 3.

 

“• CA/PEPC/04/2023 Allied Peoples Movement tsakaninta da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 4.

 

“• CA/PEPC/05/2023 Abubakar Atiku & Anor tsakani da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 2.”

 

“Wadanda aka tantance ne kawai ke da ikon shiga harabar kotun.

 

“Kuma daidaiku ne, ciki har da lauyoyi da wakilan jam’iyyu za su samu shiga cikin kwayar kotun.”

 

LEADERSHIP Hausa dai ta labarto cewa Tinubu ya samu kuri’u 8,794,726 kamar yadda INEC ga sanar da wadda hakan ya ba shi damar kayar da Atiku Abubakar na PDP mai kuri’u 6,984,520, da Peter Obi na Labour Party (LP) da ya samu kuri’u 6,101,533.

 

Jam’iyyu biyar ne suka nuna kin amincewarsu da sakamakon zaben sun hada da PDP, LP, Action Peoples Party (APP), Allied Peoples Movement (APM) ada kuma Action Alliance (AA) inda suka shigar da korafinsu a gaban kotu.

 

Jim kadan bayan fara sauraron kararrakin a watan Mayu, APP da AA sun janye korafe-korafen da suka shigar.

 

Daga cikin manya-manyan dalilan da masu korafin suka gabatar sun hada da cewa Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima ba su cancanci fitowa takarar shugaban kasa ba.

 

Sun yi ikirarin cewa Tinubu ya kasance mai laifin safaran kwayoyi a Amurka, shaidar karatunsa da ya gabatar wa INEC na bogi ne da kuma cewa Tinubu ya na da dan kasar Guinea ne.

 

Masu korafin sun cewa tun da Tinubu ya kasa samun kaso 25 cikin 100 a babban birnin tarayya FCT to bai kamata a ayyana sa a matsayin wanda ya yi nasara a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu ba.

 

A ranar 1 ga watan Agustan ne kotun sauraron kararrakin zaben mai alkalai 5 ta saurari jawabin karshe na lauyoyin Atiku da Obi.

Kotu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Kotu
Labarai

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kotu
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
Next Post
Afirka

Wannan Hadin Gwiwa Na Taimakawa Kokarin Tinkarar Sauyawar Yanayi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Kotu

Jerin Bankuna 32 Da Aka Amince Su Sayar Da Hannun Jarin Matatar Dangote

September 10, 2026
Kotu

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.