ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 7, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Kasa: Kotu Za Ta Yanke Hukunci A Ranar Laraba

Atiku, Obi Da Tinubu Za Su San Matsayarsu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotu
  •  Za A Yada Hukuncin Kai Tsaye A Gidajen Talebijin

Kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa na zaben 2023 da ya gudana, za ta yanke hukuncinta a ranar Laraba 6 ga watan Satumba kan korafe-korafen da aka shigar da ke kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu. 

 

Hukuncin da za ta yanke kan karar da jam’iyyar LP da dan takararta Peter Obi da PDP da dan takararta Atiku Abubakar da  APM da suka shigar suna kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu (APC) a matsayin shugaban Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Umarci Jakadun Nijeriya Da Su Dawo Gida

A wata sanarwar da rijistan kotun daukaka kara Umar M. Bangari Esq ya fitar a ranar Litinin, ya ce wadanda aka tantance ne kawai za su samu shiga cikin kwaryar kotun.

 

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Ya kuma ce domin tabbatar da gaskiya da yin komai a bayyane, za a yada zaman hukuncin kai tsaye a gidajen talebijin na kasa domin al’umma su bibiya kai tsaye.

 

Sanarwar ta ce, “Kotun daukaka kara tana sanar da al’umma cewa za a yanke hukunci kan kararrakin da aka gabatar a gaban kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa a ranar Laraba 6 ga watan Satumba, 2023.

 

Hukunci tsakanin “• CAREPC/03/2023 tsakanin Mr. Peter Gregory Obi & Anor tsakani da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 3.

 

“• CA/PEPC/04/2023 Allied Peoples Movement tsakaninta da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 4.

 

“• CA/PEPC/05/2023 Abubakar Atiku & Anor tsakani da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 2.”

 

“Wadanda aka tantance ne kawai ke da ikon shiga harabar kotun.

 

“Kuma daidaiku ne, ciki har da lauyoyi da wakilan jam’iyyu za su samu shiga cikin kwayar kotun.”

 

LEADERSHIP Hausa dai ta labarto cewa Tinubu ya samu kuri’u 8,794,726 kamar yadda INEC ga sanar da wadda hakan ya ba shi damar kayar da Atiku Abubakar na PDP mai kuri’u 6,984,520, da Peter Obi na Labour Party (LP) da ya samu kuri’u 6,101,533.

 

Jam’iyyu biyar ne suka nuna kin amincewarsu da sakamakon zaben sun hada da PDP, LP, Action Peoples Party (APP), Allied Peoples Movement (APM) ada kuma Action Alliance (AA) inda suka shigar da korafinsu a gaban kotu.

 

Jim kadan bayan fara sauraron kararrakin a watan Mayu, APP da AA sun janye korafe-korafen da suka shigar.

 

Daga cikin manya-manyan dalilan da masu korafin suka gabatar sun hada da cewa Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima ba su cancanci fitowa takarar shugaban kasa ba.

 

Sun yi ikirarin cewa Tinubu ya kasance mai laifin safaran kwayoyi a Amurka, shaidar karatunsa da ya gabatar wa INEC na bogi ne da kuma cewa Tinubu ya na da dan kasar Guinea ne.

 

Masu korafin sun cewa tun da Tinubu ya kasa samun kaso 25 cikin 100 a babban birnin tarayya FCT to bai kamata a ayyana sa a matsayin wanda ya yi nasara a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu ba.

 

A ranar 1 ga watan Agustan ne kotun sauraron kararrakin zaben mai alkalai 5 ta saurari jawabin karshe na lauyoyin Atiku da Obi.

Kotu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Manyan Labarai

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara
Labarai

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi
Labarai

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Next Post
Afirka

Wannan Hadin Gwiwa Na Taimakawa Kokarin Tinkarar Sauyawar Yanayi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

ADC Ta Zargi Gwamnatin Tinubu Da Jefa ‘Yan Nijeriya Miliyan 17 Cikin Yunwa

July 7, 2026
Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

Kasuwa Ce Ke Saita Tsarin Cinikayyar Sin Da EU In Ji Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin

July 6, 2026
Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

Dukkan Kabilun Kasar Sin Na Zaman Tsintsiya Madaurinki Daya

July 6, 2026
Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

Mutane 15 Sun Mutu A Hatsarin Mota A Jihar Kwara

July 6, 2026
Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

Gwamnatin Sin Ta Fara Aika Zagayen Farko Na Kayakin Agajin Gaggawa Ga Venezuela

July 6, 2026
FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

FIFA Ta Tsallake Iyakarta Dangane Da Batun Dakatarwar Balogun – UEFA

July 6, 2026
Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

Shugabannin Sin Da Madagascar Sun Yi Musayar Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 20 Da Kulla Alakar Diflomasiyya Tsakaninsu

July 6, 2026
Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

Rashin Tsaro: Kisa Ne Ya Fi Cancanta Ga ‘Yan Ta’adda Ba Gyaran Hali Ba – Ɗan Majalisa Gagdi

July 6, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.