ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shugabancin Kasa: Kotu Za Ta Yanke Hukunci A Ranar Laraba

Atiku, Obi Da Tinubu Za Su San Matsayarsu

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Kotu
  •  Za A Yada Hukuncin Kai Tsaye A Gidajen Talebijin

Kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa na zaben 2023 da ya gudana, za ta yanke hukuncinta a ranar Laraba 6 ga watan Satumba kan korafe-korafen da aka shigar da ke kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu. 

 

Hukuncin da za ta yanke kan karar da jam’iyyar LP da dan takararta Peter Obi da PDP da dan takararta Atiku Abubakar da  APM da suka shigar suna kalubalantar nasarar Bola Ahmed Tinubu (APC) a matsayin shugaban Nijeriya.

ADVERTISEMENT
  • Tinubu Ya Umarci Jakadun Nijeriya Da Su Dawo Gida

A wata sanarwar da rijistan kotun daukaka kara Umar M. Bangari Esq ya fitar a ranar Litinin, ya ce wadanda aka tantance ne kawai za su samu shiga cikin kwaryar kotun.

 

LABARAI MASU NASABA

INEC: APC da LP Ne Kaɗai Suka Cancanci Shiga Zaɓen Cike Gurbi Na Majalisar Dokokin Kebbi

Atiku Ya Buƙaci Ayyana Dokar Ta-ɓaci Kan Tsaro, Ya Yi Gargadi Kan Yawaitar Hare-Hare Kan Makarantu

Ya kuma ce domin tabbatar da gaskiya da yin komai a bayyane, za a yada zaman hukuncin kai tsaye a gidajen talebijin na kasa domin al’umma su bibiya kai tsaye.

 

Sanarwar ta ce, “Kotun daukaka kara tana sanar da al’umma cewa za a yanke hukunci kan kararrakin da aka gabatar a gaban kotun sauraron kararrakin zaben shugaban kasa a ranar Laraba 6 ga watan Satumba, 2023.

 

Hukunci tsakanin “• CAREPC/03/2023 tsakanin Mr. Peter Gregory Obi & Anor tsakani da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 3.

 

“• CA/PEPC/04/2023 Allied Peoples Movement tsakaninta da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 4.

 

“• CA/PEPC/05/2023 Abubakar Atiku & Anor tsakani da hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa da wasu 2.”

 

“Wadanda aka tantance ne kawai ke da ikon shiga harabar kotun.

 

“Kuma daidaiku ne, ciki har da lauyoyi da wakilan jam’iyyu za su samu shiga cikin kwayar kotun.”

 

LEADERSHIP Hausa dai ta labarto cewa Tinubu ya samu kuri’u 8,794,726 kamar yadda INEC ga sanar da wadda hakan ya ba shi damar kayar da Atiku Abubakar na PDP mai kuri’u 6,984,520, da Peter Obi na Labour Party (LP) da ya samu kuri’u 6,101,533.

 

Jam’iyyu biyar ne suka nuna kin amincewarsu da sakamakon zaben sun hada da PDP, LP, Action Peoples Party (APP), Allied Peoples Movement (APM) ada kuma Action Alliance (AA) inda suka shigar da korafinsu a gaban kotu.

 

Jim kadan bayan fara sauraron kararrakin a watan Mayu, APP da AA sun janye korafe-korafen da suka shigar.

 

Daga cikin manya-manyan dalilan da masu korafin suka gabatar sun hada da cewa Tinubu da Mataimakinsa Kashim Shettima ba su cancanci fitowa takarar shugaban kasa ba.

 

Sun yi ikirarin cewa Tinubu ya kasance mai laifin safaran kwayoyi a Amurka, shaidar karatunsa da ya gabatar wa INEC na bogi ne da kuma cewa Tinubu ya na da dan kasar Guinea ne.

 

Masu korafin sun cewa tun da Tinubu ya kasa samun kaso 25 cikin 100 a babban birnin tarayya FCT to bai kamata a ayyana sa a matsayin wanda ya yi nasara a zaben ranar 25 ga watan Fabrairu ba.

 

A ranar 1 ga watan Agustan ne kotun sauraron kararrakin zaben mai alkalai 5 ta saurari jawabin karshe na lauyoyin Atiku da Obi.

Kotu
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

inec
Labarai

INEC: APC da LP Ne Kaɗai Suka Cancanci Shiga Zaɓen Cike Gurbi Na Majalisar Dokokin Kebbi

June 11, 2026
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi
Manyan Labarai

Atiku Ya Buƙaci Ayyana Dokar Ta-ɓaci Kan Tsaro, Ya Yi Gargadi Kan Yawaitar Hare-Hare Kan Makarantu

June 11, 2026
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa
Manyan Labarai

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

June 10, 2026
Next Post
Afirka

Wannan Hadin Gwiwa Na Taimakawa Kokarin Tinkarar Sauyawar Yanayi A Afirka

LABARAI MASU NASABA

inec

INEC: APC da LP Ne Kaɗai Suka Cancanci Shiga Zaɓen Cike Gurbi Na Majalisar Dokokin Kebbi

June 11, 2026
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Atiku Ya Buƙaci Ayyana Dokar Ta-ɓaci Kan Tsaro, Ya Yi Gargadi Kan Yawaitar Hare-Hare Kan Makarantu

June 11, 2026
An Kafa Yanki Mafi Girma Na Hade Ayyukan Samar Da Wutar Lantarki Da Sarrafa Makamashin Hydrogen Da Adana Makamashi A Kasar Sin

An Kafa Yanki Mafi Girma Na Hade Ayyukan Samar Da Wutar Lantarki Da Sarrafa Makamashin Hydrogen Da Adana Makamashi A Kasar Sin

June 10, 2026
Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

Auren Gata: Babu Saki Sai Da Amincewar Hisbah – Daurawa

June 10, 2026
An Kaddamar Da Taron Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Fasahohi Da Masana’antun Aikin Gona na Sin Da Afirka A Kenya

An Kaddamar Da Taron Dandalin Tattauna Hadin Gwiwar Fasahohi Da Masana’antun Aikin Gona na Sin Da Afirka A Kenya

June 10, 2026
NNPCL

Zargin Sace Naira Tiriliyan 210: Majalisa Ta Bayar da Umarnin Kama Tsohon Shugaban NNPC, Mele Kyari

June 10, 2026
Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

Wakilin Sin: Bangaren Sin Yana Goyon Bayan Kasashen Afirka a Fannin Magance Matsalolin Nahiyar Bisa Hanyoyin Da Suka Dace Da Su

June 10, 2026
An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

An Kashe ’Yan Bindiga Biyu A Abuja

June 10, 2026
Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

Ko Me Ya Sa Alkaluman Rahotan Cinikayyar Waje Na Sin Suka Nuna Karuwar Nasarori Fiye Da Yadda Aka Yi Tsammani?

June 10, 2026
Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

Mamakon Ruwan Sama Da Iska Mai Ƙarfi Ya Kashe Kaka Da Jikarta A Bauchi

June 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.