• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tinubu Na Samar Da Tabarau Miliyan Biyar Ga Masu Fama Da Ciwon Ido

byIdris Aliyu Daudawa
2 years ago
Ciwon Ido

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Ranar Juma’a ta makon da ya gabata ne a Abuja Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da tsarin tallafa wa masu fama da matsalar ido, wanda hadin gwiwa ne tsakanin ma’aikatar lafiya ta tarayya da shirin tsarin lafiyar idanu ta kasa, wato gidauniyar, ‘Peek Bision’ wajen samar wa ‘yan Nijeriya fiye da miliyan biyar da suke fama da matsalar rashin gani sosai Tabarau wanda za su rika amfani da shi.

Shugaban ya tuna da yadda a karo na farko ya taba taimakawa na kusa da shi kan al’amarin da ya shafi lafiyar idanu, wannan ya say a dauki alkawari a madadin gwamnatin tarayya lokacin da aka kai ma shi ziyarar ban girma da jagora kuma shugaban gidauniyar ‘Peek Bision’, har ila yau tare da shi aka kafa gidauniyar  kulawa ta gani,Andrew Bastawrous.

  • Ma’aikatan Kiwon Lafiya 83 Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Cikin Shekara 8 – MHWUN
  • Hukumomin Sin Sun Fitar Da Wasu Ka’idoji Don Inganta Tsaron Wuraren Hakar Ma’adinai

Ya ce “Abu na farko shi ne dangane da wannan al’amari shi ne mahaifiyata Allah ya jikanta, bata lafiyar idanu hakan ne yasa bata iya gane ko wanene ni, amma dana samar mata da taimako aka kula da ita wajen ba da magani da bata Tabarau. Tambayar da ta yi mani ita ce kai nawa ne kai mani wannan abin alhairi, yanzu ya za ayi da mata da yara wadanda basu da wadanda za su  taimaka masu?.

“Sai na yi mata alkawarin zan taimaka wa mutane da yawa ta hanyar kulawa da lafiyar idanunsu ba da wasa ba, shi taimakon kulawa da lafiyar ido kyauta ne tare da yin gwaji da kuma tiyata, saboda tambayar da mahaifiyata ta yi mani da sha’awarta ta a taimakawa wajen raba wasu da cutar.

Daga karshe mun taimaka wa lafiyar idanun miliyoyin mutane a Legas za kuma za a iya lura da hakan wajen farin ciki da annashuwar da su ke ciki, domin an kara inganta masu al’amarin ganinsu ta hanyar basu Tabarau, kamar yadda Shugaban yace.

Da yake kara jaddada muhimmancin kulawa da inganta kulawa da lafiyar idanu a Nijeriya Shugaban kasa Tinubu ya nuna damuwarsa inda ya ce fiye da mutane milyan 24 suna fama da matsalolin da suka shafi idanu daban-daban.

“Lokaci ya yi wanda za mu dauki mataki saboda ai maganar gani da ji ba a wasa da al’amarinsu ba, saboda suna taka muhimmiyar wajen bunkasa tattalin arziki kamar yadda Shugaban ya ce,da  ya tuna  da wani  tsarin kula da lafiya wanda ya aiwatar  mai suna tsarin “Jigi Bola”, wanda  aka aiwatar lokacin da yake wa’adinsa na farko a matsayinsa na gwamnan Jihar Legas a shekarar 2001 inda aka kula da lafiyar idanun mutane kyauta na al’ummar Legas, inda aka  bude sabon babi na kula da lafiyar al’umma a Afirka ta yamma.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Next Post
Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version