ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tinubu Na Samar Da Tabarau Miliyan Biyar Ga Masu Fama Da Ciwon Ido

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Ciwon Ido

LABARAI MASU NASABA

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

Ranar Juma’a ta makon da ya gabata ne a Abuja Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da tsarin tallafa wa masu fama da matsalar ido, wanda hadin gwiwa ne tsakanin ma’aikatar lafiya ta tarayya da shirin tsarin lafiyar idanu ta kasa, wato gidauniyar, ‘Peek Bision’ wajen samar wa ‘yan Nijeriya fiye da miliyan biyar da suke fama da matsalar rashin gani sosai Tabarau wanda za su rika amfani da shi.

Shugaban ya tuna da yadda a karo na farko ya taba taimakawa na kusa da shi kan al’amarin da ya shafi lafiyar idanu, wannan ya say a dauki alkawari a madadin gwamnatin tarayya lokacin da aka kai ma shi ziyarar ban girma da jagora kuma shugaban gidauniyar ‘Peek Bision’, har ila yau tare da shi aka kafa gidauniyar  kulawa ta gani,Andrew Bastawrous.

  • Ma’aikatan Kiwon Lafiya 83 Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Cikin Shekara 8 – MHWUN
  • Hukumomin Sin Sun Fitar Da Wasu Ka’idoji Don Inganta Tsaron Wuraren Hakar Ma’adinai

Ya ce “Abu na farko shi ne dangane da wannan al’amari shi ne mahaifiyata Allah ya jikanta, bata lafiyar idanu hakan ne yasa bata iya gane ko wanene ni, amma dana samar mata da taimako aka kula da ita wajen ba da magani da bata Tabarau. Tambayar da ta yi mani ita ce kai nawa ne kai mani wannan abin alhairi, yanzu ya za ayi da mata da yara wadanda basu da wadanda za su  taimaka masu?.

“Sai na yi mata alkawarin zan taimaka wa mutane da yawa ta hanyar kulawa da lafiyar idanunsu ba da wasa ba, shi taimakon kulawa da lafiyar ido kyauta ne tare da yin gwaji da kuma tiyata, saboda tambayar da mahaifiyata ta yi mani da sha’awarta ta a taimakawa wajen raba wasu da cutar.

Daga karshe mun taimaka wa lafiyar idanun miliyoyin mutane a Legas za kuma za a iya lura da hakan wajen farin ciki da annashuwar da su ke ciki, domin an kara inganta masu al’amarin ganinsu ta hanyar basu Tabarau, kamar yadda Shugaban yace.

Da yake kara jaddada muhimmancin kulawa da inganta kulawa da lafiyar idanu a Nijeriya Shugaban kasa Tinubu ya nuna damuwarsa inda ya ce fiye da mutane milyan 24 suna fama da matsalolin da suka shafi idanu daban-daban.

“Lokaci ya yi wanda za mu dauki mataki saboda ai maganar gani da ji ba a wasa da al’amarinsu ba, saboda suna taka muhimmiyar wajen bunkasa tattalin arziki kamar yadda Shugaban ya ce,da  ya tuna  da wani  tsarin kula da lafiya wanda ya aiwatar  mai suna tsarin “Jigi Bola”, wanda  aka aiwatar lokacin da yake wa’adinsa na farko a matsayinsa na gwamnan Jihar Legas a shekarar 2001 inda aka kula da lafiyar idanun mutane kyauta na al’ummar Legas, inda aka  bude sabon babi na kula da lafiyar al’umma a Afirka ta yamma.

Ciwon Ido
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso
Manyan Labarai

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Next Post
Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

LABARAI MASU NASABA

Yadda Na Sayar Da Kadarori Na Don Ɗaukar Nauyin Ɗalibai A Ƙasashen Waje – Kwankwaso

Zargin Ɓata Suna: Kwankwaso Ya Yi Barazanar Neman Diyyar Naira Biliyan 10 Kan Wani Malamin Coci

June 24, 2026
Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

Li Qiang Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattalin Arzikin Duniya Na Davos Na Shekarar 2026

June 24, 2026
Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

Xi Ya Yi Kiran Daukar Matakan Zamanantar Da Aikin Gona Da Yankunan Karkara

June 24, 2026
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.