ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Shirin Tinubu Na Samar Da Tabarau Miliyan Biyar Ga Masu Fama Da Ciwon Ido

by Idris Aliyu Daudawa
3 years ago
Ciwon Ido

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

Ranar Juma’a ta makon da ya gabata ne a Abuja Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da tsarin tallafa wa masu fama da matsalar ido, wanda hadin gwiwa ne tsakanin ma’aikatar lafiya ta tarayya da shirin tsarin lafiyar idanu ta kasa, wato gidauniyar, ‘Peek Bision’ wajen samar wa ‘yan Nijeriya fiye da miliyan biyar da suke fama da matsalar rashin gani sosai Tabarau wanda za su rika amfani da shi.

Shugaban ya tuna da yadda a karo na farko ya taba taimakawa na kusa da shi kan al’amarin da ya shafi lafiyar idanu, wannan ya say a dauki alkawari a madadin gwamnatin tarayya lokacin da aka kai ma shi ziyarar ban girma da jagora kuma shugaban gidauniyar ‘Peek Bision’, har ila yau tare da shi aka kafa gidauniyar  kulawa ta gani,Andrew Bastawrous.

  • Ma’aikatan Kiwon Lafiya 83 Aka Yi Garkuwa Da Su A Katsina Cikin Shekara 8 – MHWUN
  • Hukumomin Sin Sun Fitar Da Wasu Ka’idoji Don Inganta Tsaron Wuraren Hakar Ma’adinai

Ya ce “Abu na farko shi ne dangane da wannan al’amari shi ne mahaifiyata Allah ya jikanta, bata lafiyar idanu hakan ne yasa bata iya gane ko wanene ni, amma dana samar mata da taimako aka kula da ita wajen ba da magani da bata Tabarau. Tambayar da ta yi mani ita ce kai nawa ne kai mani wannan abin alhairi, yanzu ya za ayi da mata da yara wadanda basu da wadanda za su  taimaka masu?.

“Sai na yi mata alkawarin zan taimaka wa mutane da yawa ta hanyar kulawa da lafiyar idanunsu ba da wasa ba, shi taimakon kulawa da lafiyar ido kyauta ne tare da yin gwaji da kuma tiyata, saboda tambayar da mahaifiyata ta yi mani da sha’awarta ta a taimakawa wajen raba wasu da cutar.

Daga karshe mun taimaka wa lafiyar idanun miliyoyin mutane a Legas za kuma za a iya lura da hakan wajen farin ciki da annashuwar da su ke ciki, domin an kara inganta masu al’amarin ganinsu ta hanyar basu Tabarau, kamar yadda Shugaban yace.

Da yake kara jaddada muhimmancin kulawa da inganta kulawa da lafiyar idanu a Nijeriya Shugaban kasa Tinubu ya nuna damuwarsa inda ya ce fiye da mutane milyan 24 suna fama da matsalolin da suka shafi idanu daban-daban.

“Lokaci ya yi wanda za mu dauki mataki saboda ai maganar gani da ji ba a wasa da al’amarinsu ba, saboda suna taka muhimmiyar wajen bunkasa tattalin arziki kamar yadda Shugaban ya ce,da  ya tuna  da wani  tsarin kula da lafiya wanda ya aiwatar  mai suna tsarin “Jigi Bola”, wanda  aka aiwatar lokacin da yake wa’adinsa na farko a matsayinsa na gwamnan Jihar Legas a shekarar 2001 inda aka kula da lafiyar idanun mutane kyauta na al’ummar Legas, inda aka  bude sabon babi na kula da lafiyar al’umma a Afirka ta yamma.

Ciwon Ido
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tarihin Rayuwar Galadiman Kano Alhaji Tijjani Hashim (2)
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kyamar Baƙi: An Sake Kwaso Ƴan Nijeriya 83 Daga Afirka Ta Kudu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 60 Da Kayan Aiki A Edo
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Tsohon Shugaban Ƙasa Jonathan Ya Ƙaddamar Da Ayyukan Raya Ƙasa 18 A Jihar Bauchi
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

Sabuwar Hanyar Kwacen Shafin Facebook (I)

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.