• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Firaministan Sin Ya Gana Da Shugabar Hukumar EU Da Takwaransa Na Birtaniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Firaministan sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Firaministan kasar Sin Li Qiang ya bayyana cewa, babban abin da ya shafi alakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Turai shi ne hadin gwiwa, kuma dangantakar ta kasance ta samun moriyar juna.

A ganawarsa da shugabar hukumar gudanarwar kungiyar Tarayyar Turai, Uwar gida Ursula von der Leyen a gefen taron kolin kungiyar kasashen G20, Li ya bayyana cewa, Sin da Turai, a matsayinsu na manyan rukunoni biyu na duniya, kuma manyan injuna biyu na ci gaban duniya, kamata ya yi su kara kusantowa da juna. da kuma kara inganta hadin gwiwarsu. Ya kuma yi kira ga bangarorin biyu, da su kawar da rashin tabbas dake faruwa a yanayin kasa da kasa tare da daidaita dangantakar dake tsakanin Sin da Turai.

  • AU Ta Zama Mamba Ta Dindindin A Kasashen G20 Masu Karfin Tattalin Arziki A Duniya

A nata bangaren kuwa, Von der Leyen ta ce, tun daga farkon wannan shekara, mu’amala tsakanin kasashen Turai da Sin na ci gaba da karfafa, tare da samun sakamako mai kyau. Ta kara da cewa, bangaren Turai, yana son karfafa tattaunawa da yin hadin gwiwa tare da kasar Sin a fannoni daban daban, don tinkarar sauyin yanayi tare da sauran kalubalolin da duniya ke fama da su.

Bugu da kari, firaminista Li Qiang ya bayyana a yau cewa, ya kamata kasashen Sin da Birtaniya su yi watsi da yadda ake hada batutuwan kasuwanci da tattalin arziki da siyasa da tsaro, maimakon haka su inganta tsarin tattalin arzikin duniya mai salon bude kofa, da kiyaye tsarin cinikayya tsakanin bangarori da dama bisa jagorancin kungiyar cinikayya ta duniya.

Li wanda ya bayyana hakan yayin ganawarsa da takwaransa na Birtaniya Rishi Sunak a gefen taron G20, ya ce, kasashen Sin da Birtaniya dukkansu masu goyon baya ne, masu kwarewa kuma wadanda suka ci gajiyar cinikayya cikin ‘yanci.(Ibrahim)

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: EULi Qiang
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Lallasa Kasar Sao Tome Da Ci 6-0

Next Post

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Kirkire-kirkire Na Pujiang Na Shekarar 2023 

Related

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

14 hours ago
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
Daga Birnin Sin

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

15 hours ago
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe
Daga Birnin Sin

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

16 hours ago
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

17 hours ago
Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

18 hours ago
Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci A Yi Dukkan Mai Yiwuwa Wajen Gudanar Da Ayyukan Bincike Da Ceto Bayan Aukuwar Ambaliya A Lardin Gansu

19 hours ago
Next Post
Pujiang

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin Kirkire-kirkire Na Pujiang Na Shekarar 2023 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.