• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Bada Tabbacin Inganta Daidaiton Jinsi Da Karfafa Mata.

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin jihar Kaduna ta bada tabbacin kudirinta na inganta daidaiton jinsi da kuma tafiya da Mata a dukkan shirye-shiryenta na kawo cigaba.

Mataimakiyar gwamnan jihar, Dakta Hadiza Sabuwa Balarabe ce ta bayyana haka a wani taro da aka shirya kan nauyin da ya rataya akan jjinsi mabanbanta, wanda kungiyar Mata ta Majalisar Dinkin Duniya tare da hadin guiwar Bankin Raya Afirka (AfDB) da Gidauniyar Zamani suka shirya a Kaduna.

  • Dalilin Da Ya Sa Muka Dauki Matasa 7,000 Aikin ‘Yanbanga – Gwamnatin Kaduna

Dakta Balarabe ta bayyana cewa, gwamnatin Sanata Uba Sani ta yi imanin cewa, baiwa Mata dama ba wai kawai ya dace ba ne, babbar dabara ce ta habbaka tattalin arzikin jihar wanda za su iya bunkasa ci gaba, rage talauci, da inganta hadin kan al’umma.

A cewar Dokta Hadiza Balarabe, Nijeriya ta zama cikakkiyar kasa, dole ne ta tafi da Mata don su ne rabin al’ummar kasar kuma a daina tauye su ta hanyar cin zarafinsu.

Ta nanata cewce, Mata suna fuskantar tauyewa a zamantakewa da ra’ayoyin al’adu da ke lalata karfin tattalin arzikinsu da jagoranci, kamar wariyar jinsi, tsangwama, da kuma son zuciya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Kaduna

Mataimakiyar Gwamnan, ta kara da cewa, al’amuran da suka shafi mata a koyaushe abin farin ciki ne a zuciyarta inda ta ce, “a matsayina na Mace kuma Uwa, kullum ina fuskantar wadannan kalubale. Mata ba su da cikakkiyar damar samun jarin kasuwanci, fasaha, kwarewa, da bayanai kamar yadda Maza ke samu”.

A nata jawabin, wakiliyar Majalisar Dinkin Duniya kan harkokin Mata a Nijeriya da kungiyar ECOWAS, Beatrice Eyong, ta ce kashi daya ne kacal na harkar saye da sayarwa a Nijeriya ke zuwa ga bangaren Mata ‘yan kasuwa, don haka akwai bukatar shirya taro don horaswa ta yadda za a lalubo mafita.

Kaduna

A nata jawabin, Shugabar Gidauniyar Zamani, Misis Talatu P. Zamani-Henry ta bayyana cewa, an shirya taron ne domin shawo kan kalubalen daidaiton jinsi kan samar da damar shigo da kayayyaki a jihar Kaduna da kewayenta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Daidaiton jinsiKadunaKungiyoyin mata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Sin Ta Sanya Wasu Kamfanonin Tsaron Amurka Biyu Takunkumi

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

8 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

9 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

10 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

15 hours ago
Kaduna
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

15 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

16 hours ago
Next Post
Sin

Sin Ta Sanya Wasu Kamfanonin Tsaron Amurka Biyu Takunkumi

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.