• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yanzu-yanzu: An Hana Mataimakin Gwamnan Edo Shiga Ofishinsa

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Yanzu-yanzu: An Hana Mataimakin Gwamnan Edo Shiga Ofishinsa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarin da muke samu yanzu-yanzu na nuna cewa an hana mataimakin Gwamnan jihar Edo, Comrade Philip Shaibu, shiga ofishinsa da ke Dennis Osadebey Avenue, wato fadar gwamnatin jihar da ke birnin Benin, babban birnin Jihar Edo.

Wannan wani abu ne da ke nuna yadda dangantaka ta ƙara tsami a tsakanin Gwamnan Jihar Edo Andrew Obaseki da mataimakin nasa, Shaibu.

Shaibu wanda ya tafi ofis da niyyar shiga domin gudanar da ayyuka kwatsam sai ya tarar da an kulle kofar shiga.

  • Kungiyar Kwadago (NLC) Na Shirin Tunduma Wani Sabon Yajin Aiki Mai Dogon Zango

 

Mataimakin gwamnan da hadimansa sun shafe tsawon awa guda suna tunanin ko daga baya za a bude musu kofar ofishin amma hakan ya ci tura daga bisani dole suka juya.

Labarai Masu Nasaba

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Shaibu ya yi ta kiran Gwamnan jihar Andrew Obaseki a wayar salula amma bai samu damar magana da shu ba.

Majiyoyi sun shaida cewar Shaibu ya yi magana da kwamishinan ‘yansandan jihar da daraktan ‘yansandan ciki na (DSS) inda ya shaida musu yadda aka kulle masa ofis da hanasa shiga.

Mataimakin Gwamnan ya kira kwamandan tsaron gidan gwamnatin jihar SP Ibrahim Babatunde, inda ya tambaye shi da dalili hana shi shiga ofishinsa, sai ya amsa da cewa umarni ne daga sama. Ya kara da cewa babban jami’in tsaron Gwamna (CSO) Wabba Williams, shi ne ya fi kamata a nemo domin ya yi bayanin da ya dace.

Shaibu ya kira Williams inda ya yi alkawarin cewa yana zuwa amma har tsawon lokacin da mataimakin gwamnan ya shafe yana jira bai zo ba.

“Har zuwa yanzu, ban samu wata sanarwa a hukumance kan inda zan koma ba. Illa wadanda suke da bayanin su ne ma’aikatana. Ma’aikatan gwamnati na da bayanin a hukumance amma ni ba ni da shi. A daidai lokacin nan da nake magana da kai, ina tsaye a mashigar gidan gwamnatin,” Shaibu ya shaida a lokacin da aka jiyo shi yana waya da wani mutum da ba a gane waye ba.

A makon jiya, an ce  a wata wasika daga ofishin shugaban ma’aikatan jihar, Anthony Okungbowa, da aka aike ga babban sakataren ofishin mataimakin Gwamnan, ta unarci Shaibu da ya koma sabon ofishinsa da ke lamba 7 Dennis Osadebey Avenue, GRA, a birnin Benin babban fadar jihar.

LEADERSHIP ta labarto cewa makonni biyu da suka gabata an hango alamin ofishin mataimakin gwamnan a wani sabon ofishi da ake son ya koma da ke da tazarar mitoci da fadar gwamnatin jihar, sai dai Shaibu ya nace kan cewa ba a sanar da shi cewa za a canza masa ofishi da fitar da shi daga fadar gwamnatin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BeninEdoMataimakin GwamnaShaibu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Masu Kai Wa ‘Yan Bindiga Bayanan Sirri Sun Fi Cutarwa Fiye Da ‘Yan Bindiga – Bala Kaura

Next Post

Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Related

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

1 hour ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

2 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

3 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

17 hours ago
Next Post
Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

Tsohon Sarkin Kano Sanusi II, Elumelu, Saraki Sun Isa NEW YORK Don Halartar Taron UNGA 78

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.