Manchester City ta yi rashin nasara a karon farko a kakar wasanni ta bana bayan da Newcastle ta doke ta a filin wasa na St. James Park a gasar League Cup ta bana.
City ta fara wasan ba tare da manyan ‘yan wasanta ba kamar Ederson, Haaland, Bernado Silva da Kyle Walker ba.
- Osimhen Na Shirin Karar Napoli Kan Wani Bidiyonsa Da Suka Dora Akan TikTok
- Da Alamun SAKA Ba Zai Buga Wasa Biyu Ba Saboda Raunin Da Ya Samu Arteta
Hakan yasa ta kasa tabuka abin azo a gani yayinda koci Joseph Pep Guardiola ya baiwa wasu matasan yan wasa damar buga wasan farko a Manchester City.
Aleksandar Isak ne ya zurawa Newcastle kwallo a ragar City a minti na 53 bayan dawowa hutun rabin lokaci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp