• English
  • Business News
Wednesday, September 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Taba Zuwa Gidan Yari A Kan Fim Din Da Na Shirya – Ali Ibrahim

by Rabi'at Sidi Bala
2 years ago
in Nishadi
0
Na Taba Zuwa Gidan Yari A Kan Fim Din Da Na Shirya – Ali Ibrahim
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

Daya daga cikin fitattun Jaruman, wanda ya shafe shekaru ashirin da biyar a cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, ALI IBRAHIM wanda aka fi sani da ALI DAWAYYA. Ya bayyana wa masu karatu irin kalubalen da ya fuskanta cikin masana’antar, tare da irin rawar da ya ke takawa a cikin masana’antar ta Kannywood, har ma da wasu batutuwan masu yawa wadanda suka shafi sana’arsa ta fim. Ga dai tattaunawar tare da RABI’AT SIDI BALA kamar haka:

Da farko za ka fara fadawa masu karatu cikakken sunanka tare da sunan da aka fi saninka da shi.

Sunana Ali Ibrahim wanda aka fi sani da Ali Dawayya.

Me ya sa ake kiranka da Ali Dawayya, shin kana da alaka ko dangantaka da Rukayya Dawayya ne?

Abun da ya sa ake ce mun Ali Dawayya shi ne; Akwai wani fim mai suna ‘Miras A Jo’s’ fim din kamfanin ‘Almah Production’ ni ne ‘light Man’ na fim din, sai janareto din da muke aiki da shi ya lalace na kasa gyarawa, ina ta zurga-zurga duk nayi gumi, sai Ali Nuhu ya ce; “Kanata kaiwa da dawowa ka ki zama, wannan ai kai ne Dawayya, sunan wani fim din Iyan Tama da zai fara”. Shi ne kowa ya fashe da dariya daga nan idan na zo wucewa a lokeshan din sai a yi ta yi mun dan kira ana cewa; “Dawayya”, idan na juyo sai a yi shiru, da’ na fara cewa bana son sunan sai ya zamar mun abun zolaya, amma ba ni da alaka da Rukayya Dawayya sai dai ta sama, da kuma addini daya.

Ko za ka fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinka?

Ni haifaffen garin Jo’s ne a can aka haife ni, a can nayi karatu daga nan sai ogana dan uwana Ahmad S. Nuhu na zauna a gidan yallabai Ali Nuhu ya taho da ni Kano na fara zama, amma Kano garinmu ne anan aka haifi babana a Dawakin Kudu LGA, cikin Tsakuwa. Bayan na zama dan Kano na fara koyar ‘light’ a wajen Malam Yakubu daga nan na dawo wajan Umar Gotip marigayi, daga nan sai na zama ogan kaina, ina ci gaba da rayuwata. Sai na fara sha’awar Aktin daga nan na zama furodusa na fara fim nawa na kaina mai suna ‘Akhee’, Ajo, Faraga, Sai Na Ga Ali, Kwamachala, Zafin Nema, Kifil Kwallin Mata, Bakauye, akwai uku da na manta.

Idan na fahimce ka kana so ka ce kana da alaka da Ali Nuhu da kuma Ahmad S. Nuhu ta bangaren famili kenan, ko ya batun ya ke?

Eh! ina da shi, Ahmad S. Nuhu unguwar mu daya, kuma akwai auratayya a tsakaninmu da su, shi ne ya kawo ni, Ali Nuhu a gidanshi na zauna har sanda na yi aure kuma Ali Nuhu ya dauke ni kamar shi ya haife ni, ina ci a gidan shi ina sha, sannan kuma ya mun sutura.

Wanne irin rawa ka ke takawa a cikin masana’antar Kannywood, bayan fitowa matsayin jarumi da kuma shirya fim da ka ke yi a yanzu?

Babu irin rawar da bana takawa ni ‘Light Man’ ne kuma Akto.

Za ka yi kamar shekara nawa a cikin masana’antar?

Zan kai kamar shekara 25 tun wajen 1998 na fara.

Ya batun iyaye lokacin da ka fara sanar musu kana sha’awar fara harkar fim, shin ka samu wani kalubale daga gare su ko kuwa?

A’a ban samu matsala ba fatan alkairi suka yi min, amma abokanai na ne kawai idan suka ganni sai ki ji suna mun dan kira wai Akto, haka tun raina yana baci har ya daina.

Bayan fina-finan da ka shirya naka na kanka, ko za ka iya tuna adadin fina-finan da ka fito ciki?

Gaskiya nayi fim zai kai 200.

A wanne fim ka fara fitowa?

Zubaida na kamfanin ‘FKD PRODUCTION’, shi na fara sai kuma wanda suka fito da ni duniya ta sanni.

Wanne rawa ka taka a cikin fim din, kuma ya ka ji a lokacin, musamman yadda ka ke farkon farawa a lokacin?

Sin daya na yi Ahmad S. Nuhu ya zo siyawa Abida Mohammed ‘Prem’ na ‘girft’, gaskiya lokacin da za a sa mun ‘camera’ na ji gabana ya fadi sosai tun da ban saba ba.

Ko akwai wani kalubale da ka taba fuskanta cikin masana’antar?

Gaskiya na samu kam, tun da har gidan yari na je a kan fim dina da na yi furodusin mai suna FARAGA ta dadilin fim din Jarumai 5 ne suka je gidan yari, akwai Mansoor Saddik, Falalu Dorayi, Jibrin S. Fagge, sai ni, sai Tijjani Asase.

Me ya janyo afkuwar hakan?

Na je ‘shooting’ ne wani abokina na ce ya samo min gidan da zan yi aiki, sai ya ce “to”, ashe inda zai samo min ba sa nan sun je kauye, sai ya yi wa abokinshi magana ashe abokin nashi ba shi da inda za a yi aikin sai ya yi wa wani mai gadi magana a kan ya ba mu ‘Guess Hause’ za mu yi aiki, sai mai gidan ya ce an sace masa Pijo da miliyan 10, ya yi mana sharri saboda ya taba neman wata ‘yar fim ta ki yarda da shi shi ne ya huce a kanmu.

Za mu ci gaba a mako mai zuwa


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Uwana Ne Ke Taya Ni Tallata Kayana – Sumayya Gidado

Next Post

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Binciken Duniyar Wata Mai Zuwa A Tsakanin Shekarar 2024

Related

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

3 days ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

1 week ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

2 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

3 weeks ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

1 month ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

1 month ago
Next Post
Duniyar wata

Kasar Sin Za Ta Kaddamar Da Binciken Duniyar Wata Mai Zuwa A Tsakanin Shekarar 2024

LABARAI MASU NASABA

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

An Ɗauke Wuta Sakamakon Lalacewar Babbar Tashar Lantarkin Nijeriya

September 10, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamnatin Kaduna Ta Umarci Makarantu Masu Zaman Kansu Da Su Nemi Amincewarta Kafin Ƙara Kuɗi

September 10, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Yadda Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Yaya Da Ƙannuwa Da Wasu A Zaria

September 10, 2025
Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

Kwankwaso Ya Gana Da Shugabannin NNPP A Kuros Ribas Don Tunkarar Zaɓen 2027

September 10, 2025
Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

Akwai Tara Mai Tsauri Ga Duk Wanda Ya Sare Bishiya Ba Bisa Ƙa’ida Ba – Gwamnatin Kano

September 10, 2025
majalisar kasa

Majalisa Ta Bai Wa Minista Sa’o’i 48 Ya Bayyana A Gabanta Kan Hatsarin Jirgin Abuja Zuwa Kaduna

September 10, 2025
Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

Kasar Sin Ta Zama Dandalin Karfafa Cudanya Da Cinikayya Tsakanin Kasa Da Kasa

September 9, 2025
IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

IATF 2025: Zamfara A Shirye Ta Ke Wajen Maraba Da Masu Zuba Jari – Gwamna Lawal 

September 9, 2025
An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

An Kai Jirgin Ceto Na Farko Na Kasar Sin Yankin Tsakiyar Kasar

September 9, 2025
Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

Sin Ta Samu Karuwar Kaso 9.9 Na Sabbin Kamfanoni Masu Jarin Waje A Bara

September 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.