• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Ta Samu Izinin Cafko Diezani, Ta Fara Shirye-shiryen Taso Keyarta

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Diezani

Hukumar Yaki Da Masu Yi Wa Tattalin Arzikin Kasa Zagon Kasa (EFCC), ta ce, ta samu izinin kama tsohuwar ministan albarkatun Mai, Diezani Alison-Madueke.

Hukumar ta kuma sanar da cewa, ta fara shirye-shiryen taso keyar Diezani daga can Birtaniya zuwa gida Nijeriya.

  • Zargin Bi-ta-da-ƙulli: An Hana Kotun Ɗa’ar Ma’aikata Da EFCC Da ICPC Ci Gaba Da Binciken Shugaban Yaƙi Da Rashawa Na Kano
  • EFCC Da CCB Sun Gayyaci Muhyi Magaji Rimin Gado

Rahotonni sun ce, tsohuwar ministar ta bayyana a kotun majistire ta Westminster da ke kasar Landan a ranar Litinin dangane da zargin cin hancin fam dubu 100,000.

Alkalin kotun, Michael Snow, ya amince da bayar da belin Alison-Madueke kan fam 70,000 kuma a biya nan take tare da kakaba mata wasu sharuda da suka hada da hana ta fita daga karfe 11 na dare zuwa 6 na safiya sannan kuma za a makala mata na’urar tsaro a kafarta da za ta kai rahoto kai tsaye ga jami’an tsaro da zarar ta tsallake sharuddan da kotun ta gindaya mata.

EFCC, a wata sanarwa da mukaddashin shugaban sashin yada labarai, Dele Oyewale, ya fitar, ta ce, “gurfanar da tsohowar ministan, nasara ce matuka dangane da tuhume-tuhumen zargin cin hanci da rashawa da ake mata.

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

“Duk da cewa tuhume-tuhumen da kotun London ke mata, gaba daya sun sha banban da wadanda EFCC ke mata har guda 13 da suka shafi sama da fadi da dukiyar al’umma, yana da kyau a lura da cewa dukkanin wani aikin laifi sunansa laifi, kuma ba tare da wani banbanci ba, babu wani laifi da zai tafi ba tare da an hukunta wanda ya aikata ba.

“Tuhume-tuhumen da EFCC ke wa Madueke sun shafi irin wanda ake mata a Dubai, Birtaniya, Amurka da kuma na Nijeriya.

Alison-Madueke, ‘yar shekara 63 a duniya, ta kasance wata jigo a gwamnatin tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan.

Ta yi aiki a matsayin ministan albarkatun mai daga 2010 zuwa 2015 kuma ta taba zama shugaban kungiyar kasashe masu arzikin danyen mai na duniya (OPEC).

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna
Labarai

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga
Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra
Labarai

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Next Post
Murdyk

Murdyk Ya Jefa Kwallonsa Ta Farko A Chelsea A Karawarsu Da Fulham

LABARAI MASU NASABA

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

An Rufe Taron Kolin Wuzhen Na Ayyukan Yanar Gizo Na Duniya Na Shekarar 2025

November 9, 2025
Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

Katsina United Ta Shiga Komar Hukuncin Hukumar NPFL

November 9, 2025
Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

Xi Ya Gana Da Shugabar IOC Tare Da Shugaban IOC Na Karramawa

November 9, 2025
CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

CMG Ya Cimma Yarjejeniyar Samun Iznin Watsa Shirye-shiryen Wasannin Olympics Daga Shekarar 2026 Zuwa 2032

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Na Gwaji

November 9, 2025
Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

Shugaba Xi Ya Ayyana Bude Gasar Wasanni Ta Kasa Karo Na 15

November 9, 2025
Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

Mizanin Farashin Kayan Masarufi Na Kasar Sin Ya Karu Da 0.2% A Watan Oktoba

November 9, 2025
Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

Me Ke Haddasa Yawaitar Farmakar Ƴan Wasa A Gasar Firimiyar Nijeriya

November 9, 2025
NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.