• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: ‘Yan Nijeriya Mazauna Landan Sun Nemi A Yi Wa Gwamnatin NNPP Adalci A Kano

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
NNPP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani ɓangare na murnar zagayowar Ranar Samun ‘Yanci shekaru 63 da Najeriya ta yi, ‘yan ƙasar mazauna Landan sun yi dafifi a Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan, inda su ka nemi a yi adalci a shari’ar zaɓen gwamnan Kano.

Sun taru a ofishin kowane ɗauke da kwali mai ɗauke da bayanan zargin cewa jam’iyyar APC a ƙarƙashin jagorancin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ta yi katsalandan a shari’ar da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Kano ta yanke.

  • Trump Ya Bayyana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Laifin Zamba
  • Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Mutum Hudu A Taraba

Sun riƙa ɗaga kwalaye masu ɗauke rubutu daban-daban, domin su isar da saƙon neman a yi shari’a bisa tsari na gaskiya tare da adalci ga gwamnatin NNPP a Jihar Kano.

Sun taru ne a ranar Lahadi, ranar da ta yi daidai da ranar zagayowar samun ‘yancin Najeriya.

Wasu daga cikin saƙonnin da ke rubuce a kwalayen sun haɗa da:

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Yancin kowace ƙasa dai ya dogara ne ga ‘yancin fannin shari’ar ta.”

“Kada fa a yi wa Kano fashi da ƙwacen mulki. Tinubu ya bari tsarin mulki da shari’a mai adalci ta wanzu a Kano, kuma ta yi tasiri a hukunci.”

“Tilas A Bar Wa Kano Abin Da Suka zaɓa, Ba Sauran Mulkin Rashin Adalci:Kada a sake a yi wa Abba ƙwacen nasarar zaɓen da ya yi.”

“Dole Ne Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe Su Yi Adalci – kuma kada shari’ar zaɓen Kano ta zama zakaran-gwajin-dafin zalunci.”

“A Nesanta Siyasa Daga Cikin Kotunan Mu – Kotun Ɗaukaka Ƙarar Zaɓen Kano Ta Bi Son Ran Wasu!”

“Rashin nuna ɓangaranci ga masu shari’a shi ne jigon yanke hukunci. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci da gaskiya, ba a siyasantar da hukuncin kotun zaɓe ba.”

“A Kare Dimokraɗiyya kuma a yi adalci a kotunan shari’un zaɓe. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci.”

NNPP

Jagoran masu jerin gwanon zanga-zangar, Dakta Aminu Bello, ya shaida wa ‘yan jarida cewa sun je Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan ne domin nuna rashin amincewa da hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Gwamnan Jihar Kano ta yanke, wanda ya haifar da matuƙar damuwa kan rashin adalcin da ake zargin an yi. Lamarin da ya haifar da kiraye-kirayen a yi gaskiya da adalci a Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Tarayya.

Bello ya ce hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Kano ta yanke ya jefa shakku a kan fa’ida da nagartar da ake tinƙahon samu a tsarin dimokraɗiyya.

Ya ce lallai kada a sake a ƙwace halastacciyar nasarar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ya samu.

A ƙarshe ya yi kira ga ƙungiyoyin kare haƙƙi da na dimokraɗiyya, jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyin ƙasa-da-ƙasa su sa ido sosai a kan abin da ke faruwa a Kano.

“Kuma muna kira ga hukuma ta yi ƙwaƙƙwaran bincike tare da sake bibiyar yadda aka zartas da hukuncin shari’ar zaɓen gwamna a Kano, tare da hukunta duk alƙalin da aka samu ya bada kai borin wasu masu son shirya zalunci ya hau,” Inji Bello.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun ZabeKwankwasiyyaNNPP
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yan Kasuwa 40 Sun Rasu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Kebbi

Next Post

Tinubu Ya Maye Sunan El-Rufai, Ya Aike Wa Majalisa Karin Sunan Ministoci

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

5 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

5 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

15 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

17 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

18 hours ago
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Tinubu Ya Maye Sunan El-Rufai, Ya Aike Wa Majalisa Karin Sunan Ministoci

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.