ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: ‘Yan Nijeriya Mazauna Landan Sun Nemi A Yi Wa Gwamnatin NNPP Adalci A Kano

by Sulaiman
3 years ago
NNPP

A wani ɓangare na murnar zagayowar Ranar Samun ‘Yanci shekaru 63 da Najeriya ta yi, ‘yan ƙasar mazauna Landan sun yi dafifi a Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan, inda su ka nemi a yi adalci a shari’ar zaɓen gwamnan Kano.

Sun taru a ofishin kowane ɗauke da kwali mai ɗauke da bayanan zargin cewa jam’iyyar APC a ƙarƙashin jagorancin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ta yi katsalandan a shari’ar da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Kano ta yanke.

  • Trump Ya Bayyana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Laifin Zamba
  • Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Mutum Hudu A Taraba

Sun riƙa ɗaga kwalaye masu ɗauke rubutu daban-daban, domin su isar da saƙon neman a yi shari’a bisa tsari na gaskiya tare da adalci ga gwamnatin NNPP a Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Sun taru ne a ranar Lahadi, ranar da ta yi daidai da ranar zagayowar samun ‘yancin Najeriya.

Wasu daga cikin saƙonnin da ke rubuce a kwalayen sun haɗa da:

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

“Yancin kowace ƙasa dai ya dogara ne ga ‘yancin fannin shari’ar ta.”

“Kada fa a yi wa Kano fashi da ƙwacen mulki. Tinubu ya bari tsarin mulki da shari’a mai adalci ta wanzu a Kano, kuma ta yi tasiri a hukunci.”

“Tilas A Bar Wa Kano Abin Da Suka zaɓa, Ba Sauran Mulkin Rashin Adalci:Kada a sake a yi wa Abba ƙwacen nasarar zaɓen da ya yi.”

“Dole Ne Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe Su Yi Adalci – kuma kada shari’ar zaɓen Kano ta zama zakaran-gwajin-dafin zalunci.”

“A Nesanta Siyasa Daga Cikin Kotunan Mu – Kotun Ɗaukaka Ƙarar Zaɓen Kano Ta Bi Son Ran Wasu!”

“Rashin nuna ɓangaranci ga masu shari’a shi ne jigon yanke hukunci. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci da gaskiya, ba a siyasantar da hukuncin kotun zaɓe ba.”

“A Kare Dimokraɗiyya kuma a yi adalci a kotunan shari’un zaɓe. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci.”

NNPP

Jagoran masu jerin gwanon zanga-zangar, Dakta Aminu Bello, ya shaida wa ‘yan jarida cewa sun je Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan ne domin nuna rashin amincewa da hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Gwamnan Jihar Kano ta yanke, wanda ya haifar da matuƙar damuwa kan rashin adalcin da ake zargin an yi. Lamarin da ya haifar da kiraye-kirayen a yi gaskiya da adalci a Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Tarayya.

Bello ya ce hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Kano ta yanke ya jefa shakku a kan fa’ida da nagartar da ake tinƙahon samu a tsarin dimokraɗiyya.

Ya ce lallai kada a sake a ƙwace halastacciyar nasarar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ya samu.

A ƙarshe ya yi kira ga ƙungiyoyin kare haƙƙi da na dimokraɗiyya, jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyin ƙasa-da-ƙasa su sa ido sosai a kan abin da ke faruwa a Kano.

“Kuma muna kira ga hukuma ta yi ƙwaƙƙwaran bincike tare da sake bibiyar yadda aka zartas da hukuncin shari’ar zaɓen gwamna a Kano, tare da hukunta duk alƙalin da aka samu ya bada kai borin wasu masu son shirya zalunci ya hau,” Inji Bello.

NNPP
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito
  • Sulaiman
    An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Tinubu Ya Maye Sunan El-Rufai, Ya Aike Wa Majalisa Karin Sunan Ministoci

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.