ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ranar ‘Yanci: ‘Yan Nijeriya Mazauna Landan Sun Nemi A Yi Wa Gwamnatin NNPP Adalci A Kano

by Sulaiman
3 years ago
NNPP

A wani ɓangare na murnar zagayowar Ranar Samun ‘Yanci shekaru 63 da Najeriya ta yi, ‘yan ƙasar mazauna Landan sun yi dafifi a Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan, inda su ka nemi a yi adalci a shari’ar zaɓen gwamnan Kano.

Sun taru a ofishin kowane ɗauke da kwali mai ɗauke da bayanan zargin cewa jam’iyyar APC a ƙarƙashin jagorancin tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje ta yi katsalandan a shari’ar da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Kano ta yanke.

  • Trump Ya Bayyana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Laifin Zamba
  • Wutar Lantarki Ta Yi Ajalin Mutum Hudu A Taraba

Sun riƙa ɗaga kwalaye masu ɗauke rubutu daban-daban, domin su isar da saƙon neman a yi shari’a bisa tsari na gaskiya tare da adalci ga gwamnatin NNPP a Jihar Kano.

ADVERTISEMENT

Sun taru ne a ranar Lahadi, ranar da ta yi daidai da ranar zagayowar samun ‘yancin Najeriya.

Wasu daga cikin saƙonnin da ke rubuce a kwalayen sun haɗa da:

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

“Yancin kowace ƙasa dai ya dogara ne ga ‘yancin fannin shari’ar ta.”

“Kada fa a yi wa Kano fashi da ƙwacen mulki. Tinubu ya bari tsarin mulki da shari’a mai adalci ta wanzu a Kano, kuma ta yi tasiri a hukunci.”

“Tilas A Bar Wa Kano Abin Da Suka zaɓa, Ba Sauran Mulkin Rashin Adalci:Kada a sake a yi wa Abba ƙwacen nasarar zaɓen da ya yi.”

“Dole Ne Kotun Sauraren Ƙararrakin Zaɓe Su Yi Adalci – kuma kada shari’ar zaɓen Kano ta zama zakaran-gwajin-dafin zalunci.”

“A Nesanta Siyasa Daga Cikin Kotunan Mu – Kotun Ɗaukaka Ƙarar Zaɓen Kano Ta Bi Son Ran Wasu!”

“Rashin nuna ɓangaranci ga masu shari’a shi ne jigon yanke hukunci. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci da gaskiya, ba a siyasantar da hukuncin kotun zaɓe ba.”

“A Kare Dimokraɗiyya kuma a yi adalci a kotunan shari’un zaɓe. Kanawa sun cancanci a yi masu adalci.”

NNPP

Jagoran masu jerin gwanon zanga-zangar, Dakta Aminu Bello, ya shaida wa ‘yan jarida cewa sun je Ofishin Jakadancin Najeriya da ke birnin Landan ne domin nuna rashin amincewa da hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Gwamnan Jihar Kano ta yanke, wanda ya haifar da matuƙar damuwa kan rashin adalcin da ake zargin an yi. Lamarin da ya haifar da kiraye-kirayen a yi gaskiya da adalci a Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Tarayya.

Bello ya ce hukuncin da Kotun Shari’ar Zaɓen Kano ta yanke ya jefa shakku a kan fa’ida da nagartar da ake tinƙahon samu a tsarin dimokraɗiyya.

Ya ce lallai kada a sake a ƙwace halastacciyar nasarar da Gwamna Abba Kabir Yusuf na NNPP ya samu.

A ƙarshe ya yi kira ga ƙungiyoyin kare haƙƙi da na dimokraɗiyya, jam’iyyun siyasa da ƙungiyoyin ƙasa-da-ƙasa su sa ido sosai a kan abin da ke faruwa a Kano.

“Kuma muna kira ga hukuma ta yi ƙwaƙƙwaran bincike tare da sake bibiyar yadda aka zartas da hukuncin shari’ar zaɓen gwamna a Kano, tare da hukunta duk alƙalin da aka samu ya bada kai borin wasu masu son shirya zalunci ya hau,” Inji Bello.

NNPP
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
  • Sulaiman
    Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
  • Sulaiman
    Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
  • Sulaiman
    Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Cire Tallafin Mai: Za A Fara Bai Wa Talakawa Dubu 8 Duk Wata

Tinubu Ya Maye Sunan El-Rufai, Ya Aike Wa Majalisa Karin Sunan Ministoci

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.