• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautata Dangantaka Da Sin Na Iya Taimakawa Amurka Shawo Kan Matsalar Tattalin Arzikin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyautata Dangantaka Da Sin Na Iya Taimakawa Amurka Shawo Kan Matsalar Tattalin Arzikin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Talata ne mataimakin firaministan Sin Liu He da sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen suka tattauna bisa gayyatar jami’ar ta Amurka. 

Cikin batutuwan da Jami’an biyu suka tattauna, akwai na samar da daidaito a fannin sarrafa hajoji da shigar da su kasuwanni da farfado da tattalin arzikin duniya.

  • Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

Dukkan kasashen biyu na da fasahohi da dabaru daban-daban da za su amfani juna. Kasar Sin a nata bangare, ta fi samar da kayayyaki masu rahusa, kana ta yi suna a duniya, wajen kerawa da sarrafa kayayyaki. A don haka, ’yan kasuwar Amurka za su iya amfana daga dimbin basirarta.

A nata bangare, Amurka za ta iya amfana da manufar bude kofa ta kasar Sin, har ma da babbar kasuwar da kasar ke da ita.

Sin ta sha nanata cewa kofarta a bude take ga ’yan kasuwar kasa da kasa, haka kuma a ko da yaushe, tana fadada bude kofar da rage yawan jerin bangarorin da kamfanonin waje ba za su iya zubawa jari ba, hakan ne ya sa ake ci gaba da ganin karuwar jarin kasashen waje a kasar. Haka kuma, bisa tubali mai karfi da tattalin arzikinta ke da shi, kamfanonin Amurka za su iya amfana sosai fiye ma da idan suka tsaya a kasarsu, muddun suka kiyaye dokoki da ka’idojin kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

A matsayinsu na manyan kasashe, akwai dimbin abubuwan da za su iya amfana da su daga juna, muddin Amurka ta ajiye girman kai da cin zali. A halin yanzu, ana fuskantar hauhawar farashin kayayyaki da matsalar tattalin arziki mafi muni a Amurka, hadin gwiwa da koyon dabarun kasar Sin, za su taimaka mata wajen shawo kan matsalar.

Idan ba a manta ba, Amurka ce ta fara kakkaba haraji kan wasu kayyakin Sin dake shiga kasar da fakewa da manufar tsaron kasa wajen hana kamfanoninta mu’amala da wasu daga cikin kamfanonin Sin, har ma an ga yadda a baya-bayan nan, ta zartas da dokar da ta gindaya sharuda kan audugar jihar Xinjiang.

Sai dai dukkan wannan bai sa tattalin arzikin Sin ya durkushe ba, sai ma kara samun tagomashi. Wannan manuniya ce dake cewa, ya kamata Amurka ta yi karatun ta nutsu ta duba moriyarta da na al’ummarta, ta hada hannu da Sin domin a gudu tare a tsira tare domin amfanawa al’ummunsu da ma farfado da tattalin arzikin duniya baki daya. (Faeza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Laifin Wani Ba Ya Shafar Al’umma Duka

Next Post

Ko Hukumar Kwastam Su Gyara Tsarin Dutin Motoci Ko Kuma A Daina Yi Gaba-daya —Majalisa

Related

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

1 hour ago
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama
Daga Birnin Sin

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

1 hour ago
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

21 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

22 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

23 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

23 hours ago
Next Post
Ko Hukumar Kwastam Su Gyara Tsarin Dutin Motoci Ko Kuma A Daina Yi Gaba-daya —Majalisa

Ko Hukumar Kwastam Su Gyara Tsarin Dutin Motoci Ko Kuma A Daina Yi Gaba-daya —Majalisa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

August 27, 2025
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

August 27, 2025
Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

August 27, 2025
Nijeriya Za Ta ÆŠaukaka Da Fasahar Ƙere-Æ™ere Da Tattalin Abinci – Tinubu

Nijeriya Za Ta ÆŠaukaka Da Fasahar Ƙere-Æ™ere Da Tattalin Abinci – Tinubu

August 27, 2025
Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

August 27, 2025
Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.