• Leadership Hausa
Thursday, March 23, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautata Dangantaka Da Sin Na Iya Taimakawa Amurka Shawo Kan Matsalar Tattalin Arzikin

by CMG Hausa
9 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyautata Dangantaka Da Sin Na Iya Taimakawa Amurka Shawo Kan Matsalar Tattalin Arzikin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da safiyar yau Talata ne mataimakin firaministan Sin Liu He da sakatariyar baitulmalin Amurka Janet Yellen suka tattauna bisa gayyatar jami’ar ta Amurka. 

Cikin batutuwan da Jami’an biyu suka tattauna, akwai na samar da daidaito a fannin sarrafa hajoji da shigar da su kasuwanni da farfado da tattalin arzikin duniya.

  • Saudiyya Ta Kara Wa Maniyyatan Nijeriya Kwanakin Jigilar Alhazai

Dukkan kasashen biyu na da fasahohi da dabaru daban-daban da za su amfani juna. Kasar Sin a nata bangare, ta fi samar da kayayyaki masu rahusa, kana ta yi suna a duniya, wajen kerawa da sarrafa kayayyaki. A don haka, ’yan kasuwar Amurka za su iya amfana daga dimbin basirarta.

A nata bangare, Amurka za ta iya amfana da manufar bude kofa ta kasar Sin, har ma da babbar kasuwar da kasar ke da ita.

Sin ta sha nanata cewa kofarta a bude take ga ’yan kasuwar kasa da kasa, haka kuma a ko da yaushe, tana fadada bude kofar da rage yawan jerin bangarorin da kamfanonin waje ba za su iya zubawa jari ba, hakan ne ya sa ake ci gaba da ganin karuwar jarin kasashen waje a kasar. Haka kuma, bisa tubali mai karfi da tattalin arzikinta ke da shi, kamfanonin Amurka za su iya amfana sosai fiye ma da idan suka tsaya a kasarsu, muddun suka kiyaye dokoki da ka’idojin kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

A matsayinsu na manyan kasashe, akwai dimbin abubuwan da za su iya amfana da su daga juna, muddin Amurka ta ajiye girman kai da cin zali. A halin yanzu, ana fuskantar hauhawar farashin kayayyaki da matsalar tattalin arziki mafi muni a Amurka, hadin gwiwa da koyon dabarun kasar Sin, za su taimaka mata wajen shawo kan matsalar.

Idan ba a manta ba, Amurka ce ta fara kakkaba haraji kan wasu kayyakin Sin dake shiga kasar da fakewa da manufar tsaron kasa wajen hana kamfanoninta mu’amala da wasu daga cikin kamfanonin Sin, har ma an ga yadda a baya-bayan nan, ta zartas da dokar da ta gindaya sharuda kan audugar jihar Xinjiang.

Sai dai dukkan wannan bai sa tattalin arzikin Sin ya durkushe ba, sai ma kara samun tagomashi. Wannan manuniya ce dake cewa, ya kamata Amurka ta yi karatun ta nutsu ta duba moriyarta da na al’ummarta, ta hada hannu da Sin domin a gudu tare a tsira tare domin amfanawa al’ummunsu da ma farfado da tattalin arzikin duniya baki daya. (Faeza Mustapha)

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sharhi: Laifin Wani Ba Ya Shafar Al’umma Duka

Next Post

Ko Hukumar Kwastam Su Gyara Tsarin Dutin Motoci Ko Kuma A Daina Yi Gaba-daya —Majalisa

Related

An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

11 mins ago
Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

15 mins ago
Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya
Daga Birnin Sin

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

1 hour ago
Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

2 hours ago
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum
Daga Birnin Sin

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

3 hours ago
Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?
Daga Birnin Sin

Me Ya Sa Amurka Ta Sake Rura Wuta Kan Batun Gano Asalin Annobar Covid-19?

20 hours ago
Next Post
Ko Hukumar Kwastam Su Gyara Tsarin Dutin Motoci Ko Kuma A Daina Yi Gaba-daya —Majalisa

Ko Hukumar Kwastam Su Gyara Tsarin Dutin Motoci Ko Kuma A Daina Yi Gaba-daya —Majalisa

LABARAI MASU NASABA

An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

An Yaba Da Yadda Tawagar Likitocin Kasar Sin Ta Ba Da Hidimar Kiwon Lafiya A Sudan Ta Kudu

March 23, 2023
Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

Xi Jinping Ya Kammala Ziyararsa A Kasar Rasha Cikin Nasara

March 23, 2023
Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

Matawalle Ya Karbi Faduwa, Ya Yi Fatan Alheri Ga Sabon Gwamnan Zamfara

March 23, 2023
Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

Siyasantar Da Batun Gano Asalin COVID-19 Dabara Ce Ta Boye Gaskiya

March 23, 2023
Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

Jirgin Saman Nijeriya Zai Fara Aiki Kafin Ranar 29 Ga Mayu

March 23, 2023
Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King

March 23, 2023
Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

Hadin Gwiwar Sin Da Rasha Na Da Muhimmanci Sosai Ga Duniya

March 23, 2023
Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

Ramadan: Lokutan Sahur Da Buda-baki Na Azumin Gobe A Wasu Birane

March 23, 2023
Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

Gyare-gyare Su Kan Faru Ne Bisa Sauyawar Tunanin Mutum

March 23, 2023
NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

March 23, 2023
ADVERTISEMENT
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.