• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taransifoma Ta Yi Ajalin Mutane 7 A Filato

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Filato

Al’ummar unguwar Kabong da ke Gada Biyu a karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato sun wayi gari da wani mummunar ibtila’in annoba da sanyin safiyar ranar Asabar biyo bayan bindiga da Taransifoma ta yi cikin dare da ta yi ajalin rayukan mutum 7 hadi da jikkata wasu da dama.

Wakilinmu ya labarto cewa wutar da ta tashi ta samu asali ne daga jikin na’urar rarraba wutar lantarki (taransifoma), inda mummunar gobara ta barke da ta janyo firgici da razani ga al’ummar unguwar.

  • Jerin ‘Yan Nijeriya Da Suka Shiga Sahun Fitattun Musulmi 500 A Duniya
  • Yadda Uwargida Za Ta Gyara Fuska Da Abubuwa Masu Sauki

A cewar ganau, wanda ya nemi kada a bayyana sunansa a jarida, ya ce, mutum bakwai ne suka mutu, kuma gidaje da shaguna da dama hade da kadarorin miliyoyin naira ne suka salwanta sakamakon tashin gobarar da ta samo asali daga fashewar taransifomar.

“Abun bakin ciki da takaici, biyu daga cikin mutanen da suka mutu din ‘yan gida daya ne, wanda hakan ya janyo bakin ciki da bacin rai ga ‘yan uwansu,” ya kara da cewa.

Kazalika, kamfanin rarraba wutar lantarki ta Jos (JED) ta tofa albarkacin bakinta kan annobar, inda ta ce ta kadu sosai bisa lamarin da ya faru tsakar daren ranar Asabar wanda ya shafi kwastominsu da ke amfani da na’urar rarraba wutar lantarki ta Kabong Primary a unguwar Kabong da ke kan hanyar Rububa a Jos, babban birnin jihar Filato.

LABARAI MASU NASABA

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

A sanarwar da shugaban sashin yada labarai na kamfanin, Dr. Friday Adakole Elijah, ya ce, binciken farko-farko da aka yi ya nuna cewa babban layin wuta mai dauke da balbalin wuta shi ne ya shiga layin karamin layukan wuta inda hakan ya janyo wutar ta tsallake iyakar da aka ware mata.

Ya ce, dukkanin matakan da ya dace su bi wajen tabbatar da gano hakikanin abun da ya janyo tashin wutar za su yi, kuma sun dauki matakan gaggawa na kare faruwar hakan a nan gaba.

Daga bisani kamfanin JED ya mika ta’aziyyarsa da jajantawarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da wadanda dukiyarsu ya salwanta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 
Labarai

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano
Labarai

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar
Labarai

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Next Post
Mahaifiyar Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan Ta Rasu

Mahaifiyar Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

Sashen Cinikayyar Kamfanonin Sarrafa Hajoji Na Sin Ya Bunkasa Da Kaso 4.7 Bisa Dari Cikin Watanni Tara Na Farkon Shekarar Nan

October 15, 2025
Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

Kafafen Sada Zumunta Na Zamani Suna Taimakawa Wajen Ta’azzara Matsalar Tsaro A Arewa – Yari 

October 15, 2025
Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

Nazarin CGTN: Jamaar Duniya Sun Yi Ammana Amurka Za Ta Fi Jin Jiki Daga Yakin Haraji 

October 15, 2025
Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

Kotu Ta Ɗaure Mai Horas Da ‘Yan Wasa Shekaru 8 Sakamakon Zargin Luwaɗi Da Ƙaramin Yaro A Kano

October 15, 2025
Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

Sojoji Sun Yi Juyin Mulki A Ƙasar Madagascar

October 15, 2025
Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

Shugaban Zaunannen Kwamitin Majalisar Wakilan Jama’ar Sin Ya Gana Da Mukaddashin Shugaban Majalisar Dattawan Kasar Liberia

October 15, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

Gwamnan Kaduna Ya Taya Al’Amin Murnar Nasarar Lashe Gasar Ƙirƙirar Fasaha Ta Duniya A Ƙasar Birtaniya 

October 15, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

Da Ɗumi-ɗumi: Ladan Bosso Ya Ajiye Aikin Horar Da Barau Fc 

October 15, 2025
An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

An Bude Bikin Baje Kolin Kasuwanci Na Kasa Da Kasa Na 138 A Guangzhou

October 15, 2025
sallah

Da Ɗumi-ɗumi: Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ya Ƙara Raguwa Zuwa Kashi 18.02%

October 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.