ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Taransifoma Ta Yi Ajalin Mutane 7 A Filato

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Filato

Al’ummar unguwar Kabong da ke Gada Biyu a karamar hukumar Jos ta Arewa a jihar Filato sun wayi gari da wani mummunar ibtila’in annoba da sanyin safiyar ranar Asabar biyo bayan bindiga da Taransifoma ta yi cikin dare da ta yi ajalin rayukan mutum 7 hadi da jikkata wasu da dama.

Wakilinmu ya labarto cewa wutar da ta tashi ta samu asali ne daga jikin na’urar rarraba wutar lantarki (taransifoma), inda mummunar gobara ta barke da ta janyo firgici da razani ga al’ummar unguwar.

  • Jerin ‘Yan Nijeriya Da Suka Shiga Sahun Fitattun Musulmi 500 A Duniya
  • Yadda Uwargida Za Ta Gyara Fuska Da Abubuwa Masu Sauki

A cewar ganau, wanda ya nemi kada a bayyana sunansa a jarida, ya ce, mutum bakwai ne suka mutu, kuma gidaje da shaguna da dama hade da kadarorin miliyoyin naira ne suka salwanta sakamakon tashin gobarar da ta samo asali daga fashewar taransifomar.

ADVERTISEMENT

“Abun bakin ciki da takaici, biyu daga cikin mutanen da suka mutu din ‘yan gida daya ne, wanda hakan ya janyo bakin ciki da bacin rai ga ‘yan uwansu,” ya kara da cewa.

Kazalika, kamfanin rarraba wutar lantarki ta Jos (JED) ta tofa albarkacin bakinta kan annobar, inda ta ce ta kadu sosai bisa lamarin da ya faru tsakar daren ranar Asabar wanda ya shafi kwastominsu da ke amfani da na’urar rarraba wutar lantarki ta Kabong Primary a unguwar Kabong da ke kan hanyar Rububa a Jos, babban birnin jihar Filato.

LABARAI MASU NASABA

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

A sanarwar da shugaban sashin yada labarai na kamfanin, Dr. Friday Adakole Elijah, ya ce, binciken farko-farko da aka yi ya nuna cewa babban layin wuta mai dauke da balbalin wuta shi ne ya shiga layin karamin layukan wuta inda hakan ya janyo wutar ta tsallake iyakar da aka ware mata.

Ya ce, dukkanin matakan da ya dace su bi wajen tabbatar da gano hakikanin abun da ya janyo tashin wutar za su yi, kuma sun dauki matakan gaggawa na kare faruwar hakan a nan gaba.

Daga bisani kamfanin JED ya mika ta’aziyyarsa da jajantawarsa ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu da wadanda dukiyarsu ya salwanta.

Filato
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Yaro Ya Harbe Kansa Har Lahira Bayan Mafarauci Ya Yi Sakaci Da Bindigarsa A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    An Kama Mutane 5 Da Sassan Jikin Ɗan’Adam Za Su Yi Tsafi A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mai Neman Takarar Gwamnan Bauchi, Bala Jibrin, Ya Fice Daga APC Kan Zargin Ɗoki-ɗora

MASU ALAKA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila
Manyan Labarai

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto
Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Next Post
Mahaifiyar Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan Ta Rasu

Mahaifiyar Tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Iran Ta Musanta Ikirarin Trump Tare Da Zafafa Hare-hare Kan Isra’ila

Hormuz: Iran Ta Kai Muggan Hare-hare Kan Sansanin Amurka A Jordan

September 9, 2026
ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.