• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu, ana gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa kan raya shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3, kuma kafin shirya wannan muhimmin taro, wakiliyarmu ta zanta da wasu manyan jami’an gwamnatin Najeriya a birnin Abuja, ciki har da ministan harkokin wajen kasar Yusuf Tuggar, da kakakin majalisar wakilan kasar Abbas Tajudeen.

A zantawa da ministan wajen Najeriya Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa, wannan taron yana da muhimmanci kwarai, kuma zai kawo sabon ci gaba ga Najeriya. A cewarsa gwamnatin Najeriya na mutunta dangantakarta da kasar Sin. A cikin ‘yan shekarun nan, kasashen biyu sun ci gaba da yin hadin gwiwa, tare da samun sakamako mai inganci. Najeriya ta yi imani cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” da Sin ta gabatar za ta inganta ci gaban kasashen Afirka, tana kuma fatan hada kai da Sin wajen gina al’umma mai makomar bai daya ga bil’adama.

  • Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

Tuggar ya kara da cewa, tun lokacin da kasashen Sin da Najeriya suka kulla dangantakar diplomassiya tsakaninsu, kasashen biyu suke gudanar da hadin gwiwa mai inganci a fannoni daban daban, tare da samun babban sakamako a fannonin amincewar siyasa da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya. Ya jaddada cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” tana da babbar ma’ana ga kyautata zaman rayuwar Najeriya da inganta ci gaban tattalin arzikin kasar, kana dandali na da kyau a fannin hadin gwiwar gina manyan kayayyakin more rayuwa da karfafa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka.

Shawara

Haka kuma, a nasa bangare, kakakin majalisar wakilan kasar Abbas Tajudeen, ya bayyana cewa, kasashen Najeriya da Sin dukkansu kasashe ne masu tasowa dake da kamanceceniya, kuma suna tunkarar ayyukan raya kasa da dama. Yana mai cewa, shawarar ta kawo ci gaba masu amfani da yawa ga Najeriya, kuma an sami manyan nasarori a hadin gwiwar kasashen a fannoni daban daban.

Labarai Masu Nasaba

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Abbas ya ce, Sin ta kau da matsaloli da yawa a kan hanyar samun bunkasuwa a fannonin siyasa da tattalin arziki da al’adu da sauransu, musamman a fannin kau da matsanancin talauci, aikin da Sin ta yi ya kafa wata sabuwar hanya ga kasashe masu tasowa na duniya. Kuma a bisa tallafin Sin, an kyautata manyan gine-ginen more rayuwa na Najeriya, wanda ya kara kuzari ga ci gban tattalin arzikin Najeriya, don haka Najeriya tana godiya matuka da wannan karamci.

Ban da wannan kuma, game da maganganu kan wai batun “tarkon bashi” da wasu kafofin watsa labarai na kasashen yamma suke yi kuwa, Abbas ya ce wanann ba gaskiya ba ne, bangaren Sin ya baiwa Najeriya bashin da ake bukata a fannin hadin gwiwar gina manyan kayayyakin more rayuwa, kuma bashin da kasar Sin ta baiwa Najeriya mai karancin kudin ruwa ne da kuma tsawon lokacin biya. Ya kara da cewa, Najeriya za ta tsaya tsayin daka kan shiga cikin aikin raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, don samar da makoma mai kyau ga al’ummun kasar. (Amina Xu, Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaNajeriyaShawarar ziri dayaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahara Sun Hallaka ‘Yan Sintiri 9 A Bauchi

Next Post

Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

Related

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya
Daga Birnin Sin

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

11 hours ago
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

12 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

13 hours ago
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin
Daga Birnin Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

14 hours ago
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka
Daga Birnin Sin

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

15 hours ago
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154
Daga Birnin Sin

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

16 hours ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

September 13, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

September 13, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.