ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

by Idris Aliyu Daudawa
10 months ago
Tsaro

Azuzuwan makarantu a Jihohin Benuwe, Katsina da kuma Neja yanzu an maida su wuraren kwana na muatne ƴan gudun Hijira waɗanda aka raba su da gidajensu sanadiyar ayyukan ta’addancin da ƴan ta’adda suke yi. Dubban yaran da suke waɗanɗan Jihohin yanzu basu zuwa makarantu saboda kuwa makarantun nasu an maida su, matsugunnin mutane ƴan gudun hijira.

Halin da ake ciki kuma yanzu basu san ranar da za su koma makaranta ba, irin hakan ta sa ake ganin ko shakka babu lamarin karatu zai haɗu matsala a wuraren kamar yadda rahotannin jaridar, Trust ta ƙarshen suka nuna.

A Jihar Benuwe, babu wanda zai iya faɗar yadda za’a yi da irin yadda yaran da suka isa shiga makaranta, waɗanda matsalar ƴan ta’adda ta lalata wurarensu, waɗanda kuma mutanen ne suka mamaye makaratun domin su samarwa kansu wuraren da za su riƙa kwana.

ADVERTISEMENT
  • Daga Sawaba Zuwa Asara: Baje Kolin Kasuwancin Siyasa A Kano – Auwalu Anwar
  • SDP: Fadar Shugaban Ƙasa Ta Yi Wa El-Rufai Shaguɓe Da Ayyana Shi A Matsayin Ɗan Gudun Hijirar Siyasa

Rahotanni sun nuna muatane da yawa daga rikicin ta’addanci ya fi shafar ƙananan hukumomi sun haɗa da Guma, Logo, Agatu, Kwande, Gwer ta Yamma, Apa da kuma Makurdi, yanzu al’ummar ƙananan hukumomin suna kwana ne a makarantu, hakan kuma ya kawo tsayawar harkokin da suka shafi karatu.

Wata mahaifiya, Anita Ikyur, ta ce makaranta Firamare ta NKST, a ƙaramar hukumar Logo da daɗewa ne ta zama mazauni shekarar biyar.

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Wani mahaifi, Mande Achagh, ya ce matsalar ta fi yin ƙamari a gundumarsa ta Agagbe, a ƙaramar hukumar Gwer West inda yawancin waɗanda basu da matsuguni suka samu mafaka, a wurare na musamman, makarantu, da kuma wasu gundumomi na al’umma.

“Matsalar tafi matuƙar lalacewa a Gwer ta Yamma abin kuma ya shafi makarantu sosai. Ina fatan gwamnati zata kalli lamarin domin ta ɗauki mataki, wajen samarwa mawaɗanda suka rasa matsuguni wuraren zama ta haka ‘ya’yanmu za su iya koma harkar karatu ta amfani da azuzuwansu.

“Irin matsalar da su yaran namu suke fuskanta dangane da karatunsu ba abinda za ayi wa riƙon sakainar kashi bane. Abin yana matauƙara ɓata mani rai, saboda wasu wuraren yara suna karatu ne a ƙarƙashin itatuwa, yayin da wasu kum asuka daina zuwa makaranta gaba ɗaya kamar yadda Achagh ya ce”.

Ga Jacintha Terhemen, wadda ita ɗalibi ce ‘yar makarantar Sakandare a wani harin ta’addanci da aka kai a Yelwata, ƙarƙashin ƙaramar hukumar Guma, cewa tayi duk da yake, makarantar da take abin bai shafe ta,ba saboda babu mutanen da suke kwana, amma, a, makarantun Firamare ana amfani ne, da su tare da mutanen da ta’addancin ƴan ta’adda ya raba su da garuruwan su.

“A sansanonin Ugba a Logo da Ortese a Guma, ana zuwa makaranta yayin da suma ƴan gudun Hijirar suna nan. Gwamnatin Jihar Benuwe ta ƙaddamar da wani tsari na samar da wuraren kwana masu inganci, amma hanya da za abi ita ce take da wahala sai an sa haƙuri.

An riga an sa tsari, gwamnati kuma tana neman taimako daga majalisar ɗinkin duniya da kuma Tarayyar Turai da sauran abokan tafiya masu taimakawa daga waje domin a aiwatar da shi tsarin. Aikin ana sa ran zai ci Naira Tiriliyan ɗaya, don haka abin yana buƙatar kuɗi da yawa ya kuma ƙunshi dukkan abubuwan more rayuwa waɗanda daga ƙarshe za su kawo ƙarshen matsalolin da ake fuskanta.

Neja

Makarantun da ake amfani da su a Jihar Neja wajen matsugunnin ƴan gudun Hijira sun haɗa da Central Firmare, Gwada; Central Firamare School, Kuta and Central Firamare, Erena, dukkansu a ƙaramar hukumar Shiroro.

Ɗaya daga mutanen da suka rasa matsuguni, Ahmed Almustapha, da yake sansanin Kuta, ya shaidawa Jaridar ƙarshen mako cewa wasu daga cikin yaran an maida su zuwa Model Firamare yayin da ƴan azuzuwa ne aka bar ma, sha’anin da ya shafi karatu a Central Firamare.

“Ba duka azuzuwa bane, ƴan gudun hijirar suke amfani da su ba. Wasu azuzuwan har yanzu ana amfani da su ne wajen yin karatun yara a makaranta, amma wasu Iyaye sun cire ‘ya’ansu daga Central Firamare,wurin da, ƴan gudun hijira suke zama, suka sasu a makarantar Model, Firamare.’Ya’yan mutanen da ta’addanci ya rutsa da sune kawai basu zuwa makaranta yanzu.

Wasu malaman da suke koyarwa ƴan sa kai su kan zo su koyar da su, amma yanzu sun bar zuwa.Bamu san dalilin da yasa ba,”.

Da yake makarantun da abin ya shfa ƴan gudun Hijira ne suke kwana, yawancin ƴan makarantar, an tilasta masu ne su koma wata makarantar, ko gaba ɗaya ma su bar zuwan. Wannan halin ba wai lamarin karatu kaɗai ya shafa ba,ƴan makaranta da Malamai, har ma ya maida wasu abubuwan da ake amfani, da su, sun lalace, hakan yasa cikin makarantar bai da wata sha’awar kallo . Shugaban makarantar Central Firamare, Kuta, Ya’u Ibrahim ya ce an bar shi da azuzuwa 9 kaɗai bayan kuma ga yawan ƴan makaranta da ya kai 1,360, inda yace sauran azuzuwan ƴan gudun hijira ne suke zama.

Tsaro

Ibrahim ya nuna rashin jin daɗinsa akan irin halayen su ƴan gudub hijirar, musamman ma yadda suke yin kashi a fili wanda yin hakan ba ƙaramar matsalar da take shafar lafiya bace, ga su Malamai, da kuma ƴan makaranta.

“Maganar gaskiya kasancewar ’yan gudun hijira ba ƙaramar matsala bace ga lamarin daya shafi lafiya gare mu. Suna kashi duk inda suka ga dama cikin makaranta, yanzu ko ina wari yaje yi.

“Yaran da su ma basu da matsuguni ba a sa su, makaranta ta, ba; ban san ko wane dalili bane ya sa. Babu waniɗan makarantarmu da ya bari saboda akwai ƴan gudun hijira a makarantarmu. Babbar matsalar da muke fuskanta ita ce rashin isassun azuzuwa saboda sai da muka raba ƴan makarantar uku, wato kowace rana da akwai waɗanda za su zo saboda yawansu ana kuma son a kauce ma cunkoso. Ga kuma irin yadda ake zama a sansanin wani abin damuwa ne shi ma kamar yadda ya ƙara jaddadawa”.

Katsina

An lura da cewa a Jihar Katsina da akwai yara waɗanda basu zuwa makaranta su kuma ne ke ta gararanba kan titunan manyan garuruwa a faɗin Jihar saboda lamarin da ya shafi ta’addanci da sauran laifuka. Da yake basu da wani wuri takamimi da aka ware masu domin su zauna a duk faɗin Jihar, yawanci suna zama ne da danginsu waɗanda suke a manyan garuruwa,ya yin da wasu suke zuwa makarantu ko wasu gine- gine ma mutane,irin hakan ko shakka babu yna shafar ilkimin yara a wasu makarantu.

Bada daɗewa bane mutanen da suka rasa matsugunin su daga wurare 12 daga ƙananan hukumomin Bakorı da Faskari waɗanda aka tilasta ma.

Tsaro
Idris Aliyu Daudawa
+ postsBio
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Matar Gwamnan Zamfara Ta Sha Alwashin Ci Gaba Da Tsarin Bunƙasa Ilimin Ƴa Mace
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    Hukumar Ilimin Bai-ɗaya Ta Jihar Yobe Ta Raba Kayan Karatu
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    2027:Yadda Kuɗi Da Siyasar Uban-gida Suka Daƙile Hanƙoron Matasa
  • Idris Aliyu Daudawa
    https://hausa.leadership.ng/author/idris-aliyu-daudawa/
    NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Next Post
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

LABARAI MASU NASABA

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

An Fara Gasar Tseren Dawakai Ta ‘Renewed Hope’ da Sabon Salo A Kano

June 25, 2026
APC Ta Dage Yakin Zaben Shugaban Kasarta A Kano

An Dakatar Da Shugaban APC Na Kebbi Da Kwamishina Kan Zaɓen Cike Gurbin Zuru

June 25, 2026
Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.