• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Gaza: Ana Ci Gaba Da Tir Da Kisan Fararen Hula A Harin Asibiti

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Rikicin Gaza: Ana Ci Gaba Da Tir Da Kisan Fararen Hula A Harin Asibiti
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasashen duniya na ci gaba da tofin Allah-tsine kan harin da ya janyo kisan daruruwan fararen hula a wani asibitin Gaza da ake zargin isra’ila da kaiwa.

Duk kokarin da kasashen duniya ke yi na ganin an samu maslaha kan rikicin Gaza, da alama abin ya ci tura sakamakon yadda ake dada samun rarrabuwar kawuna tsakanin masu tausayin Falasdinawa da magoya bayan Yahudun Isra’ila.

  • Zaman Lafiya: MDD Ta Fara Yunkurin Samar Da Wani Sabon Tsari A Kaduna Da Katsina
  • Sin Ta Kafa Kyakkyawan Misali A Fannin Kare Hakkokin Bil Adama

A wannan makon, an soke ganawar Shugaban Amurka Joe Biden da wasu shugabanni na Kungiyar Hadin Kan Larabawa a kasar Jordan.

Wakazalika, kasashen duniya masu tausayin Falasdinawa sun mara baya ga wani kudiri na tsagaita wuta da kasar Brazil ta gabatar wa zauren Majalizar Dinkin Duniya, sai dai Amurka ta hau kujerar na-ki a kan tabbatar da aiki da kudirin bisa abin da ta ce “ba a yi wa Isra’ila adalci ba a ciki”.

Kasashen Asiya sun yi hannun riga da na Turai kan yakin da ake yi a Zirin Gaza.

Labarai Masu Nasaba

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

…Masar Ta Bude Kan Iyakarta Da Gaza Domin Kai Taimako
Rahotanni daga kafofin yada labarai sun bayyana cewa Masar ta bude iyakarta da Gaza na wani dan lokaci domin bari a shigar da kayan agaji da kuma kyale ‘yan kasashen waje su fita.

Sai dai Ma’aikatar harkokin wajen Amurka ba ta tabbatar da rahotannin ba.
Wani sako da aka wallafa a shafin sada zumunta, ya bai wa Amurkawa da ke Gaza shawarar cewa su matsa kusa da iyakar Rafah idan suka tabbatar babu wani hadari.
A ranar Laraba ne Shugaban Amurka ya kai ziyara Isra’ila a karon farko tun bayan harin da Hamas ta kai a ranar 7 ga wannan watan.

…Harin Asibitin Gaza: Shugaban Amurka Ya Wanke Isra’ila
A lokacin da yake ganawa da Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, Shugaba Amurka, Joe Biden ya danganta harin makamai da aka kai a wani asibitin Gaza ranar Talata ga Falasdinawa cewa ba Isra’ila ba ce, bisa bayanan da ya samu inda Biden ya ce a cikin kalamansa – ‘dayan bangaren ne’.

Wannan lamari dai ya janyo ce-ce-ku-ce a tsakanin jama’a a yankin tare da soke taron da aka shirya yi tsakanin shugaba Biden da shugabannin kasashen Larabawa.

Shugaban ya jajanta wa Isra’ila game da harin da Hamas ta kai amma ya jaddada mahimmancin rage asarar fararen hula.
Wakilin Falasdinawa a Majalisar Dinkin Duniya, Riyad Mansoor ya nemi Amurka ta dakatar da Isra’ila kan kisan da take yi a Gaza, bayan harin asibitin da ake zargin ta kai ya hallaka fiye da fararen hula 450 zuwa ranar Laraba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: FalasdinuGazaHamas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Goron Juma’a

Next Post

Gwamna Uba Sani Ya Mika Ta’aziyya Ga Iyalan Marigayi Magajin Garin Zazzau

Related

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
Labarai

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

13 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

14 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

15 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

20 hours ago
Gaza
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

20 hours ago
Next Post
Magajin garin Zazzau

Gwamna Uba Sani Ya Mika Ta'aziyya Ga Iyalan Marigayi Magajin Garin Zazzau

LABARAI MASU NASABA

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.